< Ishaya 26 >

1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
Tada æe se pjevati ova pjesma u zemlji Judinoj: imamo tvrd grad; zidovi su i opkop spasenje.
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Otvorite vrata da uðe narod pravedni, koji drži vjeru.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
Ko se tebe drži, èuvaš ga jednako u miru, jer se u tebe uzda.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
Uzdajte se u Gospoda dovijeka, jer je Gospod Gospod vjeèna stijena.
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
Jer ponižuje one koji nastavaju na visini, grad visoki obara, obara ga na zemlju, obraæa ga u prah.
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
Te ga gazi noga, noge ubogih, stopala nevoljnijeh.
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
Put je pravedniku prav, ti ravniš stazu pravednome.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
I na putu sudova tvojih, Gospode, èekamo te; tvoje ime i tvoj spomen žudi duša.
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
Dušom svojom žudim tebe noæu, i duhom svojim što je u meni tražim te jutrom; jer kad su sudovi tvoji na zemlji, uèe se pravdi koji žive u vasiljenoj.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
Ako se i pomiluje bezbožnik, ne uèi se pravdi, u zemlji najpravednijoj èini bezakonje i ne gleda na velièanstvo Gospodnje.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
Gospode! ruka je tvoja visoko podignuta, a oni ne vide; vidjeæe i posramiæe se od revnosti za narod, i oganj æe proždrijeti neprijatelje tvoje.
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
Gospode! nama æeš dati mir, jer sva djela naša ti si nam uèinio.
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
Gospode Bože naš, gospodariše nad nama gospodari drugi osim tebe, ali samo tobom pominjemo ime tvoje.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
Pomriješe, neæe oživjeti, mrtvi buduæi neæe ustati, jer si ih ti pohodio i istrijebio, zatro svaki spomen njihov.
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
Gospode, umnožio si narod, umnožio si narod i proslavio si se, ali si ih zagnao na sve krajeve zemaljske.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
Gospode, u nevolji tražiše te, izlivaše pokornu molitvu kad si ih karao.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
Kao trudna žena kad hoæe da se porodi pa se muèi i vièe od bola, taki bijasmo mi pred tobom, Gospode!
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
Zatrudnjesmo, muèismo se da rodimo, i kao da rodismo vjetar, nikako ne pomogosmo zemlji, niti padoše koji žive u vasiljenoj.
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
Oživjeæe mrtvi tvoji, i moje æe mrtvo tijelo ustati. Probudite se, i pjevajte koji stanujete u prahu; jer je tvoja rosa rosa na travi, i zemlja æe izmetnuti mrtvace.
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
Hajde narode moj, uði u klijeti svoje, i zakljuèaj vrata svoja za sobom, prikrij se za èas, dokle proðe gnjev.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
Jer, gle, Gospod izlazi iz mjesta svojega da pohodi stanovnike zemaljske za bezakonje njihovo, i zemlja æe otkriti krvi svoje niti æe više pokrivati pobijenijeh svojih.

< Ishaya 26 >