< Ishaya 26 >

1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
In that dai this song schal be sungun in the lond of Juda. The citee of oure strengthe; the sauyour schal be set ther ynne, the wal and the `fore wal.
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Opene ye the yatis, and the iust folk schal entre, kepynge treuthe.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
The elde errour is gon awei; thou schalt kepe pees, pees, for thou, Lord, we hopiden in thee.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
Ye han hopid in the Lord, in euerlastynge worldis, in the Lord God, strong with outen ende.
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
For he schal bowe doun hem that dwellen an hiy, and he schal make low an hiy citee; he schal make it low `til to the erthe; he schal drawe it doun `til to the dust.
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
The foot of a pore man schal defoule it, and the steppis of nedi men schulen defoule it.
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
The weie of a iust man is riytful, the path of a iust man is riytful to go.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
And in the weie of thi domes, Lord, we suffriden thee; thi name, and thi memorial is in desir of soule.
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
My soule schal desire thee in the niyt, but also with my spirit in myn entrails; fro the morewtid Y schal wake to thee. Whanne thou schalt make thi domes in erthe, alle dwelleris of the world schulen lerne riytfulnesse.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
Do we merci to the wickid man, and he schal not lerne to do riytfulnesse; in the lond of seyntis he dide wickid thingis, and he schal not se the glorie of the Lord.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
Lord, thin hond be enhaunsid, that thei se not; puplis hauynge enuye se, and be schent, and fier deuoure thin enemyes.
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
Lord, thou schalt yyue pees to vs, for thou hast wrouyt alle oure werkis in vs.
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
Oure Lord God, lordis hadden vs in possessioun, withouten thee; oneli in thee haue we mynde of thi name.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
Thei that dien, lyue not, and giauntis risen not ayen. Therfor thou hast visityd, and hast al-to broke hem, and thou hast lost al the mynde of hem; and Lord, thou hast foryoue to a folc,
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
thou hast foryoue to a folc. Whether thou art glorified? thou hast maad fer fro thee all the endis of erthe.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
Lord, in angwisch thei souyten thee; in the tribulacioun of grutchyng thi doctryn to hem.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
As sche that conseyuede, whanne sche neiyeth sorewful to the child beryng, crieth in her sorewis, so we ben maad, Lord, of thi face.
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
We han conseyued, and we han as trauelid of child, and we han childid the spirit of helthe; we diden not riytfulnesse in erthe. Therfor the dwelleris of erthe fellen not doun; thi deed men schulen lyue,
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
and my slayn men schulen rise ayen. Ye that dwellen in dust, awake, and herie; for whi the deew of liyt is thi deew, and thou schalt drawe doun the lond of giauntis in to fallyng.
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
Go thou, my puple, entre in to thi beddis, close thi doris on thee, be thou hid a litil at a moment, til indignacioun passe.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
For lo! the Lord schal go out of his place, to visite the wickidnesse of the dwellere of erthe ayens hym; and the erthe schal schewe his blood, and schal no more hile hise slayn men.

< Ishaya 26 >