< Ishaya 26 >
1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
In that day this song will be sung in the land of Judah: We have a strong city; God has made salvation its walls and ramparts.
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Open the gates, that the righteous nation that keeps faith may enter in.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
The mind that is stayed on you, you will keep him in perfect peace, for he trusts in you.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
Trust in Yahweh forever; for in Yah, Yahweh, is an everlasting rock.
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
For he will bring down those who live proudly; the fortified city he will lay low, he will lay low to the ground; he will level it to the dust.
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
It will be trampled down by the feet of the poor and the treading of the needy.
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
The path of the righteous is level, Righteous One; the path of the righteous you make straight.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
Yes, in the path of your judgments, Yahweh, we wait for you; your name and your reputation are our desire.
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
I have longed for you in the night; yes, my spirit within me seeks you earnestly. For when your judgments come on the earth, the inhabitants of the world learn about righteousness.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
Let favor be shown to the wicked one, but he will not learn righteousness. In the land of uprightness he acts wickedly and does not see the majesty of Yahweh.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
Yahweh, your hand is lifted up, but they do not notice. But they will see your zeal for the people and be put to shame, because fire of your adversaries will devour them.
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
Yahweh, you will bring about peace for us; for indeed, you have also accomplished all our works for us.
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
Yahweh our God, other masters besides you have ruled over us; but we praise your name alone.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
They are dead, they will not live; they are deceased, they will not arise. Indeed, you came in judgment and destroyed them, and made every memory of them to perish.
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
You have increased the nation, Yahweh, you have increased the nation; you are honored; you have extended all the borders of the land.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
Yahweh, in trouble have they looked to you; they whispered prayers when your discipline was on them.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
As a pregnant woman nears the time for her to give birth, when she is in pain and cries out in her labor pains, so we have been before you, Lord.
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
We have been pregnant, we have been in labor, but it is as if we have only given birth to wind. We have not brought salvation to the earth, and the inhabitants of the world have not fallen.
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
Your dead will live; their dead bodies will arise. Awake and sing for joy, you who live in the dust; for your dew is the dew of light, and the earth will bring forth its dead.
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
Go, my people, enter into your rooms and shut your doors behind you; hide for a little while, until the indignation has passed by.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
For, look, Yahweh is about to come out of his place to punish the inhabitants of the earth for their iniquity; the earth will uncover her bloodshed, and will no longer conceal her slain.