< Ishaya 26 >
1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
Some day, [people in] Judah will sing this song: Our city [of Jerusalem] is strong! Yahweh protects our city; He is like [MET] a wall that surrounds it.
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Open the gates of the city for people who are righteous; allow people who faithfully [obey Yahweh] to enter the city.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
Yahweh, those who trust in you, those who firmly resolve to never doubt you, you will enable them to feel perfectly peaceful.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
[So] always trust in Yahweh, because Yahweh, [our God], is forever [like] [MET] a huge rock [under which we are sheltered/protected/safe].
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
He humbles proud people and destroys cities whose people are arrogant. He causes those cities to collapse into the dust/dirt.
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
[When that happens], poor and oppressed people will trample on the ruins.
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
[But as for] righteous people, Yahweh, you do what is right; [it is as though] you cause the paths where they walk to be level and smooth.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
Yahweh, by obeying your laws we show that we trust you to help us; and what we desire is that you will be honored/praised/exalted.
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
[All] through the night I [SYN] desire to know you better, and each morning I still want to be with you. [Only] when you come to judge [and punish] people who live on the earth will they learn to do what is right.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
[But] your acting kindly toward wicked people does not cause them to do what is good. [Even] in places where people do what is right, the wicked people continue to do what is evil, and they do not realize that you, Yahweh, are great.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
Yahweh, [it is as though] your fist is raised up [ready to strike them], but they do not realize that. Show them that you are very eager to help your people. If your enemies would realize that, they would be ashamed; allow your fire to burn them up [because they are] your enemies.
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
Yahweh, [we desire that] you will allow things to go well for us; everything that we have done is what you have enabled us to do.
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
Yahweh, our God, others have ruled over us, but you [MTY] are the only one whom we honor.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
Those who ruled us are [now] gone; they are dead; their spirits have left this earth, and they will not become alive [again]. You punished those rulers and got rid of them, and people do not even remember them any more.
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
Yahweh, you have enabled our nation to become great; we are more in [now], and we have more land, [so we] thank/praise you.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
Yahweh, when we were distressed, we asked you [to help us]; when you disciplined/punished us, we were able only to whisper when we prayed to you.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
Like pregnant women writhe and cry out when they are giving birth, we suffered very much, too.
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
We had severe pain, but nothing good resulted [MET] from it. We have not rescued our people [from being conquered by our enemies], and we have not given birth to children [who will rule the world correctly] (OR, not defeated the armies [that have attacked other nations].
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
But Yahweh’s people who have died will become alive [again], their corpses will become alive! Those whose bodies lie in graves will rise and shout joyfully! His light will be [like] dew that falls on his people who have died, who are [now] in the place where the dead people are, [and will cause them to become alive again].
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
But now, my people/fellow-citizens, go home and lock your doors! Hide for a short time, until [Yahweh] is no longer angry.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
Listen to this: Yahweh will come from heaven to punish [all] the people on the earth for the sins that they have committed. People will be able to see [PRS] the (blood of those/the people) who have been murdered; their murderers will no longer be able to hide.