< Ishaya 26 >
1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
In that day, shall be sung this song, in the land of Judah, —A strong city, have we! Salvation, will he set for walls and rampart,
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Open ye the gates, —That there may enter in—a righteous nation preserving fidelity.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
A purpose sustained, thou wilt guard, [saying], Prosper! Prosper! Because in thee, hath he been led to trust.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
Trust ye in Yahweh, unto futurity, —For, in Yah, Yahweh, is a rock of ages.
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
For he hath brought down the inhabitants of the height the city exalted, —He layeth it low, Layeth it low even to the ground, Levelleth it, even to the dust:
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
The foot trampleth it, —The feet of the lowly, The steps of the weak,
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
The path of a righteous man, is, even, —O Upright One! the track of a righteous man, thou makest level.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
Surely in the path of thy regulations, O Yahweh, we waited for thee, —Unto thy Name and unto thy Memorial, was there a longing of soul:
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
With my soul, longed I for thee in the night, Yea with my spirit within me, I kept on searching for thee, —For, when thy regulations [extend] to the earth, The inhabitants of the world will have learned, righteousness.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
Let favour be shewed to the lawless, he hath not learned righteousness, In a land of honest dealings, he acteth perversely, —And seeth not the splendour of Yahweh.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
O Yahweh though thy hand be lifted up, —yet do they not see, Would they might see—and turn pale at a people’s zeal, —Surely, the fire of thine enemies, must consume them!
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
O Yahweh, thou wilt ensure prosperity for us, —For even all our works, hast thou wrought for us,
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
O Yahweh, our God! Lords other than thee, have owned us, —By thyself alone, will we call upon thy Name.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
The dead, come not to life again, The shades, do not arise, —Therefore, thou hast visited and destroyed them, And caused to perish every memorial of them.
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
Thou hast increased the nation, O Yahweh, Thou hast increased the nation thou hast gotten thyself glory, Thou hast extended far, all the ends of the land.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
O Yahweh! in distress, they sought thee, —They poured out a whispered prayer, when thy chastening was upon them.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
Like as a woman with child—Draweth near to giving birth, Is in pain, Crieth out in her pangs So, were we before thee, O Yahweh; —
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
We were with child—We were in pain, As it were we brought forth wind, —Salvation, we could not accomplish for the earth, Neither were born the inhabitants of the world.
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
Thy dead, shall come to life again, My dead body, they shall arise, —Awake and shout for joy, ye that dwell in the dust For, a dew of light, is thy dew, And, earth, to the shades shall give birth.
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
Come my people, enter into thy chambers, And shut thy doors behind thee, —Hide thee as it were a little moment Till the indignation pass over.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
For lo! Yahweh, is coming forth out of his place, To visit the iniquity of earth’s inhabitant upon him, —Therefore shall the earth unveil her shed-blood, And throw a covering, no longer over her slain.