< Ishaya 26 >

1 A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
In that day shall this canticle be sung the land of Juda. Sion the city of our strength a saviour, a wall and a bulwark shall be set therein.
2 A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
Open ye the gates, and let the just nation, that keepeth the truth, enter in.
3 Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
The old error is passed away: thou wilt keep peace: peace, because we have hoped in thee.
4 Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
You have hoped in the Lord for evermore, in the Lord God mighty for ever.
5 Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
For he shall bring down them that dwell on high, the high city he shall lay low. He shall bring it down even to the ground, he shall pull it down even to the dust.
6 Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
The foot shall tread it down, the feet of the poor, the steps of the needy.
7 Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
The way of the just is right, the path of the just is right to walk in.
8 I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
And in the way of thy judgments, O Lord, we have patiently waited for thee: thy name, and thy remembrance are the desire of the soul.
9 Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
My soul hath desired thee in the night: yea, and with my spirit within me in the morning early I will watch to thee. When thou shalt do thy judgments on the earth, the inhabitants of the world shall learn justice.
10 Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
Let us have pity on the wicked, but he will not learn justice: in the land of the saints he hath done wicked things, and he shall not see the glory of the Lord.
11 Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
Lord, let thy hand be exalted, and let them not see: let the envious people see, and be confounded: and let fire devour thy enemies.
12 Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
Lord, thou wilt give us peace: for thou hast wrought all our works for us.
13 Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
O Lord our God, other lords besides thee have had dominion over us, only in thee let us remember thy name.
14 Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
Let not the dead live, let not the giants rise again: therefore hast thou visited and destroyed them, and best destroyed all their memory.
15 Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
Thou hast been favourable to the nation, O Lord, thou hast been favourable to the nation: art thou glorified? thou hast removed all the ends of the earth far off.
16 Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
Lord, they have sought after thee in distress, in the tribulation of murmuring thy instruction was with them.
17 Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
As a woman with child, when she draweth near the time of her delivery, is in pain, and crieth out in her pangs: so are we become in thy presence, O Lord.
18 Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
We have conceived, and been as it were in labour, and have brought forth wind: we have not wrought salvation on the earth, therefore the inhabitants of the earth have not fallen.
19 Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
Thy dead men shall live, my slain shall rise again: awake, and give praise, ye that dwell in the dust: for thy dew is the dew of the light: and the land of the giants thou shalt pull down into ruin.
20 Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
Go, my people, enter into thy chambers, shut thy doors upon thee, hide thyself a little for a moment, until the indignation pass away.
21 Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.
For behold the Lord will come out of his place, to visit the iniquity of the inhabitant of the earth against him: and the earth shall disclose her blood, and shall cover her slain no more.

< Ishaya 26 >