< Ishaya 25 >

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
Oh Gospod, ti si moj Bog; poviševal te bom, hvalil bom tvoje ime, kajti storil si čudovite stvari; tvoji nasveti od davnine so zvestoba in resnica.
2 Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
Kajti iz mesta si naredil kup; iz obrambnega mesta razvalino, da palača tujcev ni več mesto; ta ne bo nikoli zgrajena.
3 Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
Zato te bo močno ljudstvo proslavljalo in mesto strašnih narodov se te bo balo.
4 Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
Kajti bil si moč revnim, moč pomoči potrebnim v njihovi tegobi, zatočišče pred viharjem, senca pred vročino, ko je udar strahovitežev kakor vihar proti zidu.
5 kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
Hrup tujcev boš ponižal kakor vročino na suhem kraju, celó vročino s senco oblaka; mladika strahovitežev bo ponižana.
6 A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
Na tej gori bo Gospod nad bojevniki vsem ljudstvom pripravil praznovanje mastnih stvari, praznovanje vin na drožeh, mastnih stvari, polnih mozga, dobro prečiščenih, dolgo hranjenih vin.
7 A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
Na tej gori bo uničil obličje zagrinjala, vrženega nad vsa ljudstva in zagrinjalo, ki je razprostrto nad vsemi narodi.
8 zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
V zmagi bo pogoltnil smrt. Gospod Bog bo obrisal solze iz vseh obrazov in sramoto svojega ljudstva bo vzel proč iz vse zemlje, kajti Gospod je to govoril.
9 A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
Na ta dan bo rečeno: »Glejte! To je naš Bog; čakali smo nanj in on nas bo rešil. To je Gospod; čakali smo nanj, veseli bomo in se razveseljevali v njegovi rešitvi duše.«
10 Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
Kajti na tej gori bo počivala Gospodova roka in Moáb bo pomendran pod njim, celo kakor je slama pomendrana za gnojišče.
11 Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
Svoje roke bo razširil v njihovi sredi, kakor kdor plava razširja svoje roke za plavanje. Njihov ponos bo ponižal skupaj s pleni njihovih rok.
12 Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.
Trdnjavo visoke utrdbe tvojega obzidja bo ponižal, nizko položil in privedel k tlom, celó k prahu.

< Ishaya 25 >