< Ishaya 25 >

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
Yahweh, você é meu Deus. Eu te exaltarei! Louvarei seu nome, pois você fez coisas maravilhosas, coisas planejadas há muito tempo, em completa fidelidade e verdade.
2 Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
Pois você transformou uma cidade em uma pilha, uma cidade fortificada em uma ruína, um palácio de estranhos para não ser cidade. Ela nunca será construída.
3 Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
Portanto, um povo forte o glorificará. Uma cidade de nações fantásticas terá medo de você.
4 Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
Pois você tem sido um refúgio para os pobres, um refúgio para os necessitados em sua aflição, um refúgio contra a tempestade, uma sombra do calor, quando a explosão dos temidos é como uma tempestade contra a parede.
5 kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
Como o calor em um lugar seco, você derrubará o ruído de estranhos; como o calor pela sombra de uma nuvem, o canto dos temidos será baixado.
6 A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
Nesta montanha, Yahweh de Exércitos fará de todos os povos um banquete de carne de escolha, um banquete de vinhos de escolha, de carne de escolha cheia de tutano, de vinhos de escolha bem refinados.
7 A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
Ele destruirá nesta montanha a superfície da cobertura que cobre todos os povos, e o véu que está espalhado por todas as nações.
8 zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
Ele engoliu a morte para sempre! O Senhor Yahweh limpará as lágrimas de todos os rostos. Ele tirará a repreensão de seu povo de toda a terra, pois Yahweh o disse.
9 A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
Será dito naquele dia: “Eis que este é o nosso Deus! Esperamos por ele, e ele nos salvará! Este é Yahweh! Esperamos por ele. Ficaremos felizes e nos alegraremos com sua salvação”!
10 Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
Pois a mão de Iavé descansará nesta montanha. Moab será pisado em seu lugar, mesmo como a palha é pisada na água do monte de estrume.
11 Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
Ele estenderá suas mãos no meio dele, como quem nada estende as mãos para nadar, mas seu orgulho será humilhado junto com o ofício de suas mãos.
12 Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.
Ele derrubou a alta fortaleza de suas muralhas, baixou, e trouxe ao chão, até mesmo ao pó.

< Ishaya 25 >