< Ishaya 25 >
1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
Seigneur, vous êtes mon Dieu, je vous exalterai, je louerai votre nom, parce que vous avez fait des merveilles, que vous avez fidèlement accompli vos desseins anciens. Amen.
2 Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
Vous avez réduit une cité en un monceau de pierres, une ville puissante en une ruine; vous avez fait que la maison des étrangers ne soit pas une cité, et que jamais elle ne soit rebâtie.
3 Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
C’est pour cela qu’un peuple puissant vous louera, qu’une cité de nations redoutables vous craindra.
4 Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
Parce que vous êtes devenu une force pour le pauvre, une force pour l’indigent dans sa tribulation, un espoir contre la tempête, un ombrage contre la grande chaleur; car l’esprit des violents est de même qu’un tourbillon qui fond sur une muraille.
5 kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
Comme une grande chaleur dans la soif, vous humilierez l’insolence tumultueuse des étrangers; et comme par la chaleur brûlante du soleil sous un nuage, vous ferez sécher la race des puissants.
6 A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
Et le Seigneur des armées fera à tous les peuples sur cette montagne un festin de viandes grasses, un festin de vin, de viandes moelleuses, d’un vin pur de toute he.
7 A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
Il jettera sur cette montagne la chaîne même qui hait tous les peuples, et la toile qu’il avait ourdie pour envelopper toutes les nations.
8 zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
Il précipitera la mort pour jamais; et il enlèvera, le Seigneur Dieu, les larmes de toute face, et il enlèvera l’opprobre de son peuple de la terre entière; parce que le Seigneur a parlé.
9 A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
Et son peuple dira en ce jour-là: Voici, c’est notre Dieu, celui-ci; nous l’avons attendu et il nous sauvera; c’est le Seigneur, nous l’avons attendu patiemment, nous exulterons, et nous nous réjouirons dans son salut.
10 Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
Parce que la main du Seigneur se reposera sur cette montagne, et Moab sera brisé sous lui, comme sont brisées des pailles par un chariot.
11 Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
Et il étendra ses mains sous lui, comme les étend celui qui nage pour nager; et il humiliera sa gloire, en brisant ses mains.
12 Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.
Les remparts de tes hautes montagnes s’écrouleront, et ils seront abattus et renversés par terre jusque dans la poussière.