< Ishaya 25 >

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
Yahweh, you are my God; I will honor you and praise you [MTY]. You do wonderful things; you said long ago that you would do those things, and now you have done them like you said that you would.
2 Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
[Sometimes] you have caused cities to become heaps of rubble, cities that had strong walls around them. You have caused palaces in foreign countries to disappear; they will never be rebuilt.
3 Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
Therefore, people in powerful nations will declare that you are very great, and people in nations [whose leaders are] ruthless/cruel will revere you.
4 Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
Yahweh, you are [like] [SIM] a strong tower where poor people can (find refuge/be safe), a place where needy people can go when they are distressed. [You are like] [MET] a place where people can find refuge in a storm and where they can be shaded from the hot sun. Ruthless/Cruel [people] oppress us; they are like [SIM] a storm beating against a wall,
5 kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
and like [SIM] [the intense] heat in the desert. [But] you cause the roaring of people in foreign nations to cease. Like the air cools when a cloud comes overhead, you stop ruthless/cruel [people] from singing songs boasting about their being very great.
6 A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
Here in Jerusalem, the Commander of the armies of angels will prepare a wonderful feast for all the people [of the world]. It will be a banquet with plenty of good meat and fine well-aged [DOU] wine.
7 A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
[People here are] sad; their being sad is [like] a dark cloud that hangs over them, like they experience when someone dies. But Yahweh will enable them to quit being sad.
8 zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
He will get rid of death forever! Yahweh our God will cause people to no longer mourn because someone has died. And he will stop other people insulting and making fun of his land and [us] his people. [That will surely happen because] Yahweh has said it!
9 A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
At that time, [people] will proclaim, “Yahweh is our God! We trusted in him, and he rescued us! Yahweh, in whom we trusted, has done it; we should rejoice because of his saving/rescuing [us]!”
10 Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
Yahweh [MTY] will protect and bless Jerusalem. [But] he will crush [the people in the land of] Moab; they will be like [SIM] straw that is trampled in the manure [and left to rot].
11 Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
Yahweh will push down the people of Moab like [SIM] a swimmer pushes [the water] with his hands. He will cause them to cease being proud, and he will show that all the things that they have done are worthless.
12 Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.
The high walls [around the cities] in Moab will be torn down; they will be demolished and fall into the dust/dirt.

< Ishaya 25 >