< Ishaya 25 >

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
O LORD, Thou art my God, I will exalt Thee, I will praise Thy name, for Thou hast done wonderful things; even counsels of old, in faithfulness and truth.
2 Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
For Thou hast made of a city a heap, of a fortified city a ruin; a castle of strangers to be no city, it shall never be built.
3 Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
Therefore shall the strong people glorify Thee, the city of the terrible nations shall fear Thee.
4 Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
For Thou hast been a stronghold to the poor, a stronghold to the needy in his distress, a refuge from the storm, a shadow from the heat; for the blast of the terrible ones was as a storm against the wall.
5 kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
As the heat in a dry place, Thou didst subdue the noise of strangers; as the heat by the shadow of a cloud, the song of the terrible ones was brought low.
6 A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
And in this mountain will the LORD of hosts make unto all peoples a feast of fat things, a feast of wines on the lees, of fat things full of marrow, of wines on the lees well refined.
7 A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
And He will destroy in this mountain the face of the covering that is cast over all peoples, and the veil that is spread over all nations.
8 zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
He will swallow up death for ever; and the Lord GOD will wipe away tears from off all faces; and the reproach of His people will He take away from off all the earth; for the LORD hath spoken it.
9 A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
And it shall be said in that day: 'Lo, this is our God, for whom we waited, that He might save us; this is the LORD, for whom we waited, we will be glad and rejoice in His salvation.'
10 Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
For in this mountain will the hand of the LORD rest, and Moab shall be trodden down in his place, even as straw is trodden down in the dunghill.
11 Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
And when he shall spread forth his hands in the midst thereof, as he that swimmeth spreadeth forth his hands to swim, his pride shall be brought down together with the cunning of his hands.
12 Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.
And the high fortress of thy walls will He bring down, lay low, and bring to the ground, even to the dust.

< Ishaya 25 >