< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Si, Herren gör landet tomt och öde, och omstörtar hvad deruti är, och förströr dess inbyggare.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
Och Prestenom går såsom folkena; herranom såsom tjenarenom, frune såsom tärnone; så honom som säljer, som honom som köper, honom som lånar, såsom honom som borgar; kräfvarenom, såsom gäldenärenom;
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
Ty landet skall varda tomt och skinnadt; ty Herren hafver detta sagt.
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
Landet står jämmerliga, och förderfvas; jordenes krets förvanskas och förderfvas; de högste af folket i landena förminskas.
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
Landet är oskärdt vordet af sina inbyggare; förty att de öfverträda lagen, och förvandla buden, och låta det eviga förbundet fara.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
Derföre uppfräter förbannelse landet; ty de som deruti bo, förskylla det; derföre borttorkas landsens inbyggare, så att fögo folk qvart blifver.
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
Vinet försvinner, vinträt förvissnar, och alle de, som af hjertat glade voro, sucka.
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
Fröjd af trummor håller upp, de gladas lust är ute; harpors fröjd hafver en ända.
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
Man sjunger intet, der man vin dricker, och god dryck är bitter dem som dricka honom.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
Den tomme staden är nederbruten; all hus äro tillsluten, så att ingen går derin.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
Man klagar efter vin på gatone, all glädje är borto, all landsens fröjd är sin väg.
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
Icke annat än förödelse är blifvet i stadenom, och portarna stå öde.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
Ty det går i landena och med folkena, lika som när ett oljoträ afplockadt är; såsom när man efterhämtar, då vinanden ute är.
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
De samme upphäfva deras röst och lofva, och glädjas öfver Herrans härlighet ifrå hafvet.
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
Så priser nu Herran i dalomen; på hafsens öar Herrans Israels Guds Namn.
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
Vi höre lofsång ifrå jordenes ända, den Rättfärdiga till äro; och jag måste säga: Hvi är jag dock så mager? Hvi är jag dock så mager? Ve mig! ty föraktarena förakta, ja, föraktarena förakta.
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
Derföre kommer öfver eder, landsens inbyggare, förskräckelse, grop och snara.
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
Och om en undflydde för förskräckelsens rop, så faller han dock likväl uti gropena. Kommer han utu gropene, så varder han dock fången i snarone; ty fenstren i höjdene äro upplåtna, och jordenes grundvalar bäfva.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
Landena varder illa gångandes; det skall icke trifvas, utan måste förfalla.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
Landet skall raga hit och dit, såsom en drucken, och bortfördt varda, lika som en hydda; ty dess missgerningar trycka det, så att det falla måste, och kan icke blifva.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
På den tiden skall Herren besöka det höga herrskapet, som i höjdene är, och jorderikes Konungar, som på jordene äro;
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
Att de skola tillhopasamkas såsom ett knippe till gropena, och skola förslutne varda uti fångahuse, och efter lång tid åter besökte varda.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
Och månen skall skämma sig, och solen blygas; då Herren Zebaoth skall Konung varda på berget Zion, och i Jerusalem, och för sina äldsta i härlighet.

< Ishaya 24 >