< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
اینک خداوند زمین را خالی و ویران می کند، و آن را واژگون ساخته، ساکنانش را پراکنده می‌سازد.۱
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
و مثل قوم، مثل کاهن و مثل بنده، مثل آقایش و مثل کنیز، مثل خاتونش و مثل مشتری، مثل فروشنده و مثل قرض دهنده، مثل قرض گیرنده و مثل سودخوار، مثل سود دهنده خواهد بود.۲
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
و زمین بالکل خالی و بالکل غارت خواهد شد زیرا خداوند این سخن را گفته است.۳
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
زمین ماتم می‌کند و پژمرده می‌شود. ربع مسکون کاهیده و پژمرده می‌گردد، شریفان اهل زمین کاهیده می‌شوند.۴
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
زمین زیرساکنانش ملوث می‌شود زیرا که از شرایع تجاوزنموده و فرایض را تبدیل کرده و عهد جاودانی راشکسته‌اند.۵
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
بنابراین لعنت، جهان را فانی کرده است و ساکنانش سزا یافته‌اند لهذا ساکنان زمین سوخته شده‌اند و مردمان، بسیار کم باقی‌مانده‌اند.۶
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
شیره انگور ماتم می‌گیرد و مو کاهیده می‌گردد وتمامی شاددلان آه می‌کشند.۷
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
شادمانی دفها تلف شده، آواز عشرت کنندگان باطل و شادمانی بربطها ساکت خواهد شد.۸
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
شراب را با سرودهانخواهند آشامید و مسکرات برای نوشندگانش تلخ خواهد شد.۹
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
قریه خرابه منهدم می‌شود وهر خانه بسته می‌گردد که کسی داخل آن نتواندشد.۱۰
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
غوغایی برای شراب در کوچه‌ها است. هرگونه شادمانی تاریک گردیده و سرور زمین رفع شده است.۱۱
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
ویرانی در شهر باقی است ودروازه هایش به هلاکت خرد شده است.۱۲
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
زیرا که در وسط زمین در میان قوم هایش چنین خواهدشد مثل تکانیدن زیتون و مانند خوشه هایی که بعد از چیدن انگور باقی می‌ماند.۱۳
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
اینان آواز خود را بلند کرده، ترنم خواهندنمود و درباره کبریایی خداوند از دریا صداخواهند زد.۱۴
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
از این جهت خداوند را در بلادمشرق و نام یهوه خدای اسرائیل را درجزیره های دریا تمجید نمایید.۱۵
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
از کرانهای زمین سرودها را شنیدیم که عادلان را جلال باد. اما گفتم: وا حسرتا، وا حسرتا، وای بر من! خیانت کاران خیانت ورزیده، خیانت کاران به شدت خیانت ورزیده‌اند.۱۶
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
‌ای ساکن زمین ترس و حفره و دام بر تو است.۱۷
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
و واقع خواهد شد که هرکه از آواز ترس بگریزد به حفره خواهد افتاد وهر‌که از میان حفره برآید گرفتار دام خواهد شدزیرا که روزنه های علیین باز شده و اساسهای زمین متزلزل می‌باشد.۱۸
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
زمین بالکل منکسرشده. زمین تمام از هم پاشیده و زمین به شدت متحرک گشته است.۱۹
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
زمین مثل مستان افتان وخیزان است و مثل سایه بان به چپ و راست متحرک و گناهش بر آن سنگین است. پس افتاده است که بار دیگر نخواهد برخاست.۲۰
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
و در آن روز واقع خواهد شد که خداوندگروه شریفان را بر مکان بلند ایشان و پادشاهان زمین را بر زمین سزا خواهد داد.۲۱
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
و ایشان مثل اسیران در چاه جمع خواهند شد و درزندان بسته خواهند گردید و بعد از روزهای بسیار، ایشان طلبیده خواهند شد.۲۲
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
و ماه خجل و آفتاب رسوا خواهد گشت زیرا که یهوه صبایوت در کوه صهیون و در اورشلیم و به حضور مشایخ خویش، با جلال سلطنت خواهدنمود.۲۳

< Ishaya 24 >