< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Khangela, uThixo uzabhidliza umhlaba utshabalale; uzawuchitha, ahlakaze abahlala kuwo.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
Kuzafanana okuzenziwa kumphristi kuzenziwa lasebantwini, okuzenziwa enkosini kuzenziwa lasencekwini, okuzenziwa enkosikazini kuzenziwa lasencekukazini, okuzenziwa kumthengisi kuzenziwa lakumthengi, okuzenziwa kowebolekayo kuzenziwa lakumebolekisi, okuzenziwa kokweledayo kuzenziwa lakokweledisayo.
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
Umhlaba uzatshabalaliswa nya uphangwe uqedwe du. UThixo uselikhulumile ilizwi leli.
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
Umhlaba uyoma ubune, umhlaba uyahodoza ubune, abaphakemeyo bomhlaba bayahodoza!
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
Umhlaba ungcoliswa ngabantu bawo. Kabayilalelanga imithetho, beqe imilayo bephula isivumelwano esingapheliyo.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
Ngakho-ke umhlaba uchithwa yisiqalekiso; abantu bawo kumele bahlupheke ngenxa yokona kwabo. Ngakho abantu abahlala emhlabeni bayatshiswa, njalo balutshwana kakhulu abaseleyo.
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
Iwayini elitsha liyaphela, amavini ayabuna; bonke abenza umsindo bejabula bayabubula.
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
Ukukhala kwamagedla kuthulisiwe, umsindo wabajabulayo usuphelile, ichacho lentokozo selithule.
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
Kabasanathi iwayini behlabela, utshwala buyababa kubanathi babo.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
Idolobho elidilikileyo litshabalele; iminyango yezindlu zonke ivalekile.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
Emigwaqweni bakhalela iwayini, yonke intokozo iba yikudana, ukujabula konke kuphelile emhlabeni.
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
Idolobho lisele selingamanxiwa, isango lalo libhidlizwe laba yizicucu.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
Kuzakuba njalo emhlabeni laphakathi kwezizwe, njengalapho isihlahla somʼoliva sinyikinywa, loba njengezithelo ezitholwa emva kokuvunwa kwamavini.
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
Baphakamisa amazwi abo, bahlabele ngentokozo; bememezela ubukhosi bukaThixo bengasentshonalanga.
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
Ngakho-ke dumisani uThixo empumalanga; phakamisani uThixo, uNkulunkulu ka-Israyeli, ezihlengeni zolwandle.
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
Sizwa ukuhlabelela okuvela emikhawulweni yomhlaba: “Udumo kalube koLungileyo.” Kodwa mina ngathi, “Ngiyacikizeka, ngiyacikizeka! Maye mina! Abakhohlisi bayaceba! Ngenkohliso abakhohlisi bayaceba!”
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
Ukwesaba, igodi lomjibila kulilindele, lina bantu basemhlabeni.
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
Loba ngubani obalekela umsindo wokwesaba uzawela egodini; loba ngubani ophumayo egodini uzabanjwa ngumjibila. Amasango asezulwini avuliwe, izisekelo zomhlaba ziyanyikinyeka.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
Umhlaba usubhidlikile, umhlaba usudabuke phakathi, umhlaba usunyikinywe impela.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
Umhlaba udiyazela njengesidakwa, uzunguzeka njengendlu kulesiphepho; siwusinda kangaka isono sokuhlamuka kwawo uze uwe, awuyikuvuka futhi.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
Ngalolosuku uThixo uzajezisa amabutho asemazulwini phezulu lamakhosi emhlabeni ngaphansi.
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
Bazabuthelwa ndawonye njengezibotshwa zibotshiwe emgodini oyintolongo. Bazavalelwa entolongweni bajeziswe emva kwensuku ezinengi.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
Inyanga izayangeka, ilanga libelenhloni; ngoba uThixo uSomandla uzabusa ngenkazimulo phezu kweNtaba iZiyoni laphakathi kweJerusalema, laphambi kwabadala bakhona.

< Ishaya 24 >