< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Voici, l'Éternel vide le pays et le dévaste, et il en bouleverse la surface et en disperse les habitants.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
Et il en sera du sacrificateur comme du peuple, du maître comme du serviteur, de la maîtresse comme de la servante, du vendeur comme de l'acheteur, du prêteur comme de l'emprunteur, du créancier comme du débiteur.
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
Le pays sera vidé, et il sera mis au pillage, car l'Éternel a prononcé cette parole.
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
Le pays gémit et languit, le monde est dans la langueur et dans le deuil, les sommités du peuple du pays languissent.
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
Or le pays était profané par ses habitants; car ils violaient les lois, transgressaient les ordonnances, rompaient l'alliance éternelle.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
Aussi, la malédiction dévore le pays et les habitants en portent la peine; c'est pourquoi les habitants du pays sont consumés, et il n'en survit qu'un petit nombre.
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
Le moût est triste, et la vigne dépérit; tous ceux qui avaient le cœur joyeux, soupirent.
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
Les joies des cymbales ont cessé, et le bruit de la gaieté a fini, les joies de la harpe ont cessé.
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
On ne boit plus de vin en chantant, la cervoise est amère aux buveurs.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
La ville en ruine est une cité déserte; toute maison est fermée, on n'y entre plus.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
Sur le vin on se lamente dans les rues, toute joie est disparue, et la gaieté du pays est bannie.
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
Ce qui reste dans la ville, c'est la désolation, et les portes brisées sont en ruines.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
Car il en est dans le pays, au milieu des peuples, comme à l'abattis des olives, comme au grappillage quand la vendange est finie.
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
Les autres élèvent leurs voix, poussent des cris d'allégresse; depuis la mer ils célèbrent la majesté de l'Éternel.
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
Aussi glorifiez l'Éternel dans l'orient, dans les îles de la mer le nom de l'Éternel, Dieu d'Israël.
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
Des bouts de la terre nous entendons des chants: « Gloire au juste! » Mais moi je dis: Ruine sur moi! ruine sur moi! malheur à moi! Les pillards pillent, et les pillards enlèvent du pillage.
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
Effroi, et fosse, et filet devant toi, habitant du pays!
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
Qui fuit l'effroi, tombe dans la fosse, et qui se tire de la fosse, se prend au filet, car les écluses des lieux très-hauts s'ouvrent, et les fondements de la terre branlent.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
La terre se brise, la terre se rompt, la terre est ébranlée.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
La terre chancelle comme un homme ivre, elle se balance comme un hamac, et son péché pèse sur elle, et elle tombe pour ne pas se relever.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
Et en ce même jour, l'Éternel châtiera l'armée des lieux très-hauts dans les lieux très-hauts, et les rois de la terre sur la terre,
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
et ils seront réunis captifs dans la prison, et enfermés dans le cachot, et après un long temps ils seront châtiés.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
Alors la lune sera honteuse et le soleil confus; car l'Éternel des armées règne sur la montagne de Sion et à Jérusalem, et devant ses anciens resplendira la gloire.

< Ishaya 24 >