< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Voici, l'Eternel s'en va rendre le pays vide, et l'épuiser; et il en renversera le dessus, et dispersera ses habitants.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
Et tel sera le Sacrificateur que le peuple; tel le maître que son serviteur; telle la dame que sa servante; tel le vendeur que l'acheteur; tel celui qui prête que celui qui emprunte; tel le créancier, que le débiteur.
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
Le pays sera entièrement vidé, et entièrement pillé; car l'Eternel a prononcé cet arrêt.
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
La terre mène deuil, elle est déchue; le pays habité est devenu languissant, il est déchu; les plus distingués du peuple de la terre sont languissants.
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
Le pays a été profané par ses habitants, qui marchent sur lui; parce qu'ils ont transgressé les lois, ils ont changé les ordonnances, et ont enfreint l'alliance éternelle.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
C'est pourquoi l'exécration du serment a dévoré le pays, et ses habitants ont été mis en désolation; à cause de cela les habitants du pays sont brûlés, et peu de gens sont demeurés de reste.
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
Le vin excellent a mené deuil, la vigne languit, tous ceux qui avaient le cœur joyeux soupirent.
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
La joie des tambours a cessé; le bruit de ceux qui s'égayent est fini; la joie de la harpe a cessé.
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
On ne boira plus de vin avec des chansons; la cervoise sera amère à ceux qui la boivent.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
La ville défigurée a été ruinée, toute maison est fermée, tellement que personne n'y entre.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
La clameur est dans les places à cause que le vin [a manqué], toute la joie est tournée en obscurité, l'allégresse du pays s'en est allée.
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
La désolation est demeurée dans la ville, et la porte est frappée d'une ruine éclatante.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
Car il arrivera au milieu de la terre, et parmi les peuples, comme quand on secoue l'olivier, et [comme] quand on grappille après avoir achevé de vendanger.
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
Ceux-ci élèveront leur voix, ils se réjouiront avec chant de triomphe, et s'égayeront de devers la mer, à cause de la majesté de l'Eternel.
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
C'est pourquoi glorifiez l'Eternel dans les vallées, le Nom de l'Eternel, le Dieu d'Israël, dans les Iles de la mer.
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
Nous avions entendu du bout de la terre des cantiques [qui portaient] que le Juste était plein de noblesse; mais j'ai dit: Maigreur sur moi! maigreur sur moi! Malheur à moi! les perfides ont agi perfidement; et ils ont imité la mauvaise foi des perfides.
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
La frayeur, la fosse, et le piège sont sur toi, habitant du pays.
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
Et il arrivera que celui qui s'enfuira à cause du bruit de la frayeur, tombera dans la fosse; et celui qui sera remonté hors de la fosse, sera attrapé au filet; car les bondes d'en haut sont ouvertes, et les fondements de la terre tremblent.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
La terre s'est entièrement brisée, la terre s'est entièrement écrasée, la terre s'est entièrement remuée de sa place.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
La terre chancellera entièrement comme un homme ivre, et sera transportée comme une loge, et son forfait s'appesantira sur elle, tellement qu'elle tombera, et ne se relèvera plus.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
Et il arrivera en ce jour-là, que l'Eternel visitera dans un lieu élevé l'armée superbe, et les Rois de la terre, sur la terre.
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
Et ils seront assemblés en troupe comme des prisonniers dans une fosse; et ils seront enfermés dans une prison, et après plusieurs jours ils seront visités.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
La lune rougira, et le soleil sera honteux, quand l'Eternel des armées régnera en la montagne de Sion, et à Jérusalem; et ce ne sera que gloire en la présence de ses Anciens.

< Ishaya 24 >