< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Some day, Yahweh is going to destroy everything on the earth. He will devastate it and cause it to become a desert and scatter its people.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
He will scatter everyone— priests and common people, servants and their masters, maids and their mistresses, buyers and sellers, lenders and borrowers, people who owe money and people who are owed money.
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
Nothing that is worth anything will be left on earth; everything valuable will be destroyed. [That will surely happen because] Yahweh has said it.
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
[Everything on] the earth will dry up and die [DOU]; its important people will become weak and unimportant.
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
The earth has become unacceptable to Yahweh because the people who live on it have disobeyed his laws; they have rejected the agreement that he intended to last forever.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
Therefore, [Yahweh] will curse the earth; the people who live on it must be punished because of the sins that they have committed. They will be destroyed by fire, and [only a] few people will remain [alive].
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
The grapevines will wither, and there will be no [grapes to make] wine. All [the people] who were previously happy will then groan and mourn.
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
People will no longer play cheerful songs with tambourines, people will no longer play joyfully on their harps, and people will no longer shout noisily [during their celebrations].
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
People will no longer sing while they drink wine, and [all] their alcoholic drinks will taste bitter.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
[Towns and] cities will be desolate; every house will be locked to prevent thieves from entering.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
[Mobs] will gather in the streets, wanting wine; no one on the earth will be happy [DOU] any more.
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
Cities will be ruined and [all] their gates will be battered/broken into pieces.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
It will be like that all over the earth: [there will only be a few people still alive], like what happens when [workers] beat all the olives off a tree [and there are only a few left], [or] when they harvest the grapes and there are only a few left [on the vines].
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
But [those who are left alive] will sing joyfully; people [in nations] to the west [of Israel] will declare that Yahweh is very great;
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
people in nations to the east [of Israel will also] praise Yahweh [MTY]; in countries across the sea, people will praise Yahweh, the God whom we Israelis [worship].
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
We will hear [people] in the most distant places on the earth singing praise to [Yahweh], the [truly] righteous one. But [now], I am [SYN] very sad. Weep for me, [because] I have become thin and weak. Terrible things are happening! Treacherous [people still] betray/deceive others everywhere [DOU].
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
You people all over the earth, you will be terrified, and you will fall into deep pits and traps/snares.
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
Those who [try to] flee because they are terrified will fall into [deep] pits, and those who climb out of the pits will be caught by traps/snares. The sky will split open and torrents [SIM] [of rain will fall]; the foundations of the earth will shake.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
The earth will split apart and be shattered; it will shake violently.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
[It will be as though] the earth will stagger like [SIM] a drunk; it will shake like [SIM] a hut [shakes in a windstorm]. It will collapse and not [be able to] rise again, [because] the guilt of the people who rebel [against Yahweh] is very great.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
At that time, Yahweh will punish the [wicked] powerful beings in the skies and the wicked kings on the earth.
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
They will [all] be gathered together and thrown into a dungeon/pit. They will be shut/locked in that dungeon/pit, and later they will be punished.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
At that time the light of the moon and the sun will be lessened; [it will be as though] they are ashamed [in the presence of] Yahweh, because he, the Commander of the armies of angels, will rule gloriously (on Zion Hill/in Jerusalem), in the presence of the leaders [of his people].

< Ishaya 24 >