< Ishaya 24 >
1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Behold, the LORD maketh the earth empty, and maketh it waste, and turneth it upside down, and scattereth abroad the inhabitants thereof.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
And it shall be, as with the people, so with the priest; as with the servant, so with his master; as with the maid, so with her mistress; as with the buyer, so with the seller; as with the lender, so with the borrower; as with the taker of usury, so with the giver of usury to him.
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
The earth shall be utterly emptied, and utterly spoiled; for the LORD hath spoken this word.
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
The earth mourneth and fadeth away, the world languisheth and fadeth away, the lofty people of the earth do languish.
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
The earth also is polluted under the inhabitants thereof; because they have transgressed the laws, changed the ordinance, broken the everlasting covenant.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
Therefore hath the curse devoured the earth, and they that dwell therein are found guilty: therefore the inhabitants of the earth are burned, and few men left.
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
The new wine mourneth, the vine languisheth, all the merryhearted do sigh.
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
The mirth of tabrets ceaseth, the noise of them that rejoice endeth, the joy of the harp ceaseth.
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
They shall not drink wine with a song; strong drink shall be bitter to them that drink it.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
The city of confusion is broken down: every house is shut up, that no man may come in.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
There is a crying in the streets because of the wine; all joy is darkened, the mirth of the land is gone.
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
In the city is left desolation, and the gate is smitten with destruction.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
For thus shall it be in the midst of the earth among the peoples, as the shaking of an olive tree, as the grape gleanings when the vintage is done.
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
These shall lift up their voice, they shall shout; for the majesty of the LORD they cry aloud from the sea.
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
Wherefore glorify ye the LORD in the east, even the name of the LORD, the God of Israel, in the isles of the sea.
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
From the uttermost part of the earth have we heard songs, glory to the righteous. But I said, I pine away, I pine away, woe is me! the treacherous dealers have dealt treacherously; yea, the treacherous dealers have dealt very treacherously.
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
Fear, and the pit, and the snare, are upon thee, O inhabitant of the earth.
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
And it shall come to pass, that he who fleeth from the noise of the fear shall fall into the pit; and he that cometh up out of the midst of the pit shall be taken in the snare: for the windows on high are opened, and the foundations of the earth do shake.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
The earth is utterly broken, the earth is clean dissolved, the earth is moved exceedingly.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
The earth shall stagger like a drunken man, and shall be moved to and fro like a hut; and the transgression thereof shall be heavy upon it, and it shall fall, and not rise again.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
And it shall come to pass in that day, that the LORD shall punish the host of the high ones on high, and the kings of the earth upon the earth.
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
And they shall be gathered together, as prisoners are gathered in the pit, and shall be shut up in the prison, and after many days shall they be visited.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
Then the moon shall be confounded, and the sun ashamed; for the LORD of hosts shall reign in mount Zion, and in Jerusalem, and before his ancients gloriously.