< Ishaya 24 >

1 Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
Behold, Jehovah makes the earth empty, and makes it waste, and turns it upside down, and scatters abroad the inhabitants of it.
2 zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
And it shall be, as with the people, so with the priest, as with the servant, so with his master, as with the maid, so with her mistress, as with the buyer, so with the seller, as with the creditor, so with the debtor, as with the taker of interest, so with the giver of interest to him.
3 Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
The earth shall be utterly emptied, and utterly laid waste, for Jehovah has spoken this word.
4 Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
The earth mourns and fades away. The world languishes and fades away. The lofty people of the earth languish.
5 Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
The earth also is polluted under the inhabitants of it, because they have transgressed the laws, violated the statutes, broken the everlasting covenant.
6 Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
Therefore the curse has devoured the earth, and those who dwell in it are found guilty. Therefore the inhabitants of the earth are burned, and few men left.
7 Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
The new wine mourns. The vine languishes. All the merry-hearted do sigh.
8 Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
The mirth of tambourine ceases. The noise of those who rejoice ends. The joy of the harp ceases.
9 Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
They shall not drink wine with a song. Strong drink shall be bitter to those who drink it.
10 Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
The waste city is broken down. Every house is shut up, that no man may come in.
11 A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
There is a crying in the streets because of the wine. All joy is darkened. The mirth of the land is gone.
12 An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
Desolation is left in the city, and the gate is smitten with destruction.
13 Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
For thus shall it be in the midst of the earth among the peoples, as the shaking of an olive tree, as the gleanings when the vintage is done.
14 Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
These shall lift up their voice. They shall shout. For the majesty of Jehovah they cry aloud from the sea.
15 Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
Therefore glorify ye Jehovah in the east, even the name of Jehovah, the God of Israel, in the isles of the sea.
16 Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
From the outermost part of the earth we have heard songs. Glory to the righteous. But I said, I pine away, I pine away. Woe is me! The treacherous have dealt treacherously, yea, the treacherous have dealt very treacherously.
17 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
Fear, and the pit, and the snare, are upon thee, O inhabitant of the earth.
18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
And it shall come to pass, that he who flees from the noise of the fear shall fall into the pit, and he who comes up out of the midst of the pit shall be taken in the snare. For the windows on high are opened, and the foundations of the earth tremble.
19 An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
The earth is utterly broken. The earth is torn apart. The earth is shaken violently.
20 Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
The earth shall stagger like a drunken man, and shall sway to and fro like a hammock. And the transgression of it shall be heavy upon it, and it shall fall, and not rise again.
21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
And it shall come to pass in that day, that Jehovah will punish the host of the high ones on high, and the kings of the earth upon the earth.
22 Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
And they shall be gathered together as prisoners are gathered in the pit, and shall be shut up in the prison. And after many days they shall be visited.
23 Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.
Then the moon shall be confounded, and the sun ashamed, for Jehovah of hosts will reign in mount Zion and in Jerusalem. And glory shall be before his elders.

< Ishaya 24 >