< Ishaya 23 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
Utsaga om Tyrus. Jämren eder, I Tarsis-skepp! Ty det är ödelagt, utan hus och utan gäster; från kittéernas land når dem budskapet härom.
2 Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
Sitten stumma, I kustlandets invånare! Köpmän från Sidon, sjöfarande män, uppfyllde dig;
3 A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
av Sihors säd och Nilflodens skördar skaffade du dig vinning, i det du for över stora vatten och drev handel därmed bland folken.
4 Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
Men stå där nu med skam, du Sidon; ty så säger havet, havets fäste: "Så är jag då utan avkomma och har icke fött några barn, icke uppfött ynglingar, icke fostrat jungfrur."
5 Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
När man får höra detta i Egypten, då bävar man vid ryktet om Tyrus.
6 Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
Dragen bort till Tarsis och jämren eder, I kustlandets invånare.
7 Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
Är detta eder glada stad, hon den urgamla, som av sina fötter bars till fjärran land, för att gästa där?
8 Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
Vem beslöt detta över Tyrus, henne som delade ut kronor, vilkens köpmän voro furstar, vilkens krämare voro stormän på jorden?
9 Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
HERREN Sebaot var den som beslöt det, för att slå ned all den stolta härligheten och ödmjuka alla stormän på jorden.
10 Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
Bred nu ut dig över ditt land såsom Nilfloden, du dotter Tarsis; du bär ingen boja mer.
11 Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
Han räckte ut sin hand över havet, han kom konungariken att darra; HERREN bjöd om Kanaans fästen att de skulle ödeläggas.
12 Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
Han sade: "Du skall ej allt framgent få leva i fröjd, du kränkta jungfru, du dotter Sidon. Stå upp och drag bort till kittéernas land; dock, ej heller där får du ro.
13 Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
Se, kaldéernas land, folket som förr ej var till, de vilkas land Assyrien gjorde till boning åt öknens djur, de resa där sina belägringstorn och omstörta stadens platser och göra den till en grushög.
14 Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
Jämren eder, I Tarsis-skepp, ty edert fäste är förstört."
15 A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
På den tiden skall Tyrus ligga förgätet i sjuttio år, såsom rådde där alltjämt en och samma konung; men efter sjuttio år skall det gå med Tyrus, såsom det heter i visan om skökan:
16 “Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
"Tag din harpa och gå omkring i staden, du förgätna sköka; spela vackert och sjung flitigt, så att man kommer ihåg dig."
17 A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
Ty efter sjuttio år skall HERREN se till Tyrus, och det skall åter få begynna att taga emot skökolön och bedriva otukt med jordens alla konungariken i den vida världen.
18 Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.
Men hennes handelsförvärv och vad hon får såsom skökolön skall vara helgat åt HERREN; det skall icke läggas upp och icke gömmas, utan de som bo inför HERRENS ansikte skola av hennes handelsförvärv hava mat till fyllest och präktiga kläder.

< Ishaya 23 >