< Ishaya 23 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
وحی درباره صور ای کشتیهای ترشیش ولوله نمایید زیراکه بحدی خراب شده است که نه خانه‌ای و نه مدخلی باقی‌مانده. از زمین کتیم خبر به ایشان رسیده است.۱
2 Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
‌ای ساکنان ساحل که تاجران صیدون که از دریا عبور می‌کنند تو را پرساخته‌اند آرام گیرید.۲
3 A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
و دخل او از محصول شیحور و حصاد نیل بر آبهای بسیار می‌بود پس اوتجارت گاه امت‌ها شده است.۳
4 Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
‌ای صیدون خجل شو زیرا که دریا یعنی قلعه دریا متکلم شده، می‌گوید درد زه نکشیده‌ام و نزاییده‌ام وجوانان را نپرورده‌ام و دوشیزگان را تربیت نکرده‌ام.۴
5 Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
چون این خبر به مصر برسد از اخبارصور بسیار دردناک خواهند شد.۵
6 Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
‌ای ساکنان ساحل دریا به ترشیش بگذرید وولوله نمایید.۶
7 Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
آیا این شهر مفتخر شما است که قدیمی و از ایام سلف بوده است و پایهایش او رابه‌جای دور برده، تا در آنجا ماوا گزیند؟۷
8 Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
کیست که این قصد را درباره صور آن شهر تاج بخش که تجار وی سروران و بازرگانان او شرفای جهان بوده‌اند نموده است.۸
9 Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
یهوه صبایوت این قصد رانموده است تا تکبر تمامی جلال را خوار سازد وجمیع شرفای جهان را محقر نماید.۹
10 Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
‌ای دختر ترشیش از زمین خود مثل نیل بگذر زیرا که دیگر هیچ بند برای تو نیست.۱۰
11 Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
اودست خود را بر دریا دراز کرده، مملکتها رامتحرک ساخته است. خداوند درباره کنعان امرفرموده است تا قلعه هایش را خراب نمایند.۱۱
12 Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
وگفته است: ای دوشیزه ستم رسیده و‌ای دخترصیدون دیگر مفتخر نخواهی شد. برخاسته، به کتیم بگذر اما در آنجا نیز راحت برای تو نخواهدبود.۱۲
13 Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
اینک زمین کلدانیان که قومی نبودند وآشور آن را به جهت صحرانشینان بنیاد نهاد. ایشان منجنیقهای خود را افراشته، قصرهای آن را منهدم و آن را به خرابی مبدل خواهند ساخت.۱۳
14 Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
‌ای کشتیهای ترشیش ولوله نمایید زیرا که قلعه شما خراب شده است.۱۴
15 A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
و در آن روز واقع خواهد شد که صور، هفتاد سال مثل ایام یک پادشاه فراموش خواهدشد و بعد از انقضای هفتاد سال برای صور مثل سرود زانیه خواهد بود.۱۵
16 “Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
‌ای زانیه فراموش شده بربط را گرفته، در شهر گردش نما. خوش بنواز وسرودهای بسیار بخوان تا به یاد آورده شوی.۱۶
17 A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
وبعد از انقضای هفتاد سال واقع می‌شود که خداوند از صور تفقد خواهد نمود و به اجرت خویش برگشته با جمیع ممالک جهان که بر روی زمین است زنا خواهد نمود.۱۷
18 Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.
و تجارت واجرت آن برای خداوند وقف شده ذخیره و اندوخته نخواهد شد بلکه تجارتش برای مقربان درگاه خداوند خواهد بود تا به سیری بخورند ولباس فاخر بپوشند.۱۸

< Ishaya 23 >