< Ishaya 23 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
Prophétie sur Tyr. Gémissez, navires de Tarsis, car elle est détruite! Plus de maisons! On n'y entre plus! La nouvelle leur en vient du pays de Kittim.
2 Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
Soyez stupéfaits, habitants de la côte, toi qui étais remplie par les marchands de Sidon, qui parcourent la mer!
3 A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
A travers les grandes eaux, les grains du Shichor, les moissons du Nil, étaient son revenu; elle était le marché des nations.
4 Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
Sois honteuse, ô Sidon! Car la mer, la forteresse de la mer, a parlé ainsi: Je n'ai point été en travail, je n'ai point enfanté, je n'ai point nourri de jeunes gens, ni élevé de jeunes filles.
5 Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
Quand la nouvelle parviendra en Égypte, ils trembleront aux nouvelles de Tyr.
6 Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
Passez à Tarsis; gémissez, habitants du rivage!
7 Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
Est-ce là votre joyeuse cité, dont l'origine remonte au jours anciens? Ses pieds la portent au loin pour habiter en étrangère!
8 Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
Qui a résolu ces choses contre Tyr, la distributrice de couronnes, dont les marchands étaient des princes, dont les trafiquants étaient les grands de la terre?
9 Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
L'Éternel des armées l'a résolu, pour abaisser toute gloire orgueilleuse, pour humilier tous les grands de la terre.
10 Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
Parcours ton pays, pareille au fleuve, fille de Tarsis; plus de liens qui te retiennent!
11 Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
L'Éternel a étendu sa main sur la mer, il a fait trembler les royaumes. Il a donné ordre contre Canaan, pour détruire ses forteresses.
12 Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
Il a dit: Tu ne continueras plus à te réjouir, fille de Sidon, vierge déshonorée! Lève-toi, passe au pays de Kittim; là même, tu n'auras point de repos.
13 Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
Vois le pays des Caldéens, peuple qui naguère n'était pas: Assur assigna ce pays aux habitants du désert. Ils dressent leurs tours, ils détruisent les palais de Tyr, ils la mettent en ruines.
14 Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
Gémissez, navires de Tarsis! Car votre forteresse est détruite.
15 A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
En ce temps-là, Tyr sera mise en oubli soixante-dix ans, le temps de la vie d'un roi. Au bout de soixante-dix ans, il en sera de Tyr comme de la courtisane dont parle la chanson:
16 “Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
“Prends la harpe, fais le tour de la ville, courtisane oubliée! Touche bien les cordes; multiplie les chants; afin qu'on se souvienne de toi! “
17 A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
Et au bout de soixante-dix ans, l'Éternel visitera Tyr; elle retournera à ses gains impurs, elle se prostituera sur la face du monde avec tous les royaumes de la terre.
18 Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.
Mais ses profits et ses gains impurs seront consacrés à l'Éternel: il n'en sera rien accumulé, ni réservé. Car ses profits seront à ceux qui habitent devant la face de l'Éternel, pour les nourrir abondamment et les vêtir avec magnificence.

< Ishaya 23 >