< Ishaya 23 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
Profeti imod Tyrus. Hyler, I Tharsis's Skibe! thi den er ødelagt, saa der ikke er et Hus, og saa at ingen kommer derind; fra Kithims Land kundgøres dette for dem.
2 Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
Tier, I Indbyggere paa Øen, som Zidons Købmænd, der fore over Havet, fyldte!
3 A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
Over de store Vande blev Sæden ved Sikor, Høsten ved Strømmen, dens Indkomst; og den var Hedningernes Stapelstad.
4 Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
Skam dig, Zidon! thi Havet, Befæstningen ved Havet, siger: Jeg har ikke været i Fødselsnød og har ikke født og ikke opdraget unge Karle og ikke opfødt Jomfruer.
5 Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
Saa si art Rygtet naar Ægypten, skulle de blive bange ved Rygtet om Tyrus.
6 Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
Farer over til Tharsis, hyler, I Indbyggere paa Øen!
7 Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
Er dette eders jublende Stad, den, hvis Udspring er fra Oldtid, den, hvis Fødder føre den ud, langt bort til at være fremmed?
8 Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
Hvo har besluttet dette over Tyrus, den, som uddelte Kroner, den, hvis Købmænd vare Fyrster, den, hvis Kræmmere vare de herligste paa Jorden?
9 Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
Den Herre Zebaoth har besluttet det for at nedslaa al denne dejlige Herlighed, for at gøre de herlige paa Jorden ringe.
10 Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
Far igennem dit Land som Strømmen, du Tharsis's Datter! der er intet Bælte ydermere.
11 Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
Han udrakte sin Haand over Havet, han bragte Rigerne til at bæve; Herren bød om Kanaan at ødelægge dens Befæstninger.
12 Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
Og han sagde: Du skal ikke blive ved at fryde dig ydermere, du voldtagne Jomfru, Zidons Datter! gør dig rede, drag hen over til Kithim; men end ikke der skal du have Hvile.
13 Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
Se, Kaldæernes Land — der er Folket, som ikke længe har været til, Assur har grundlagt det for Ørkenens Børn — de have oprejst Vagttaarne, nedbrudt dens Paladser, gjort den til en Stenhob.
14 Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
Hyler, I Tharsis's Skibe! thi eders Befæstning er forstyrret.
15 A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
Og det skal ske paa den Dag, da skal Tyrus blive glemt halvfjerdsindstyve Aar, som ere en Konges Dage; men naar halvfjerdsindstyve Aar ere til Ende, skal det gaa Tyrus efter Skøgevisen:
16 “Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
„Tag Harpe, gak omkring i Staden, du glemte Skøge! leg smukt paa Strenge, syng meget, paa det du maa ihukommes!”
17 A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
Og det skal ske, efter at halvfjerdsindstyve Aar ere til Ende, da skal Herren besøge Tyrus, og den skal komme til sin Fortjeneste igen og bole med alle Riger paa Jorden, paa Jordens Kreds.
18 Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.
Men dens Købmandsskab og dens Fortjeneste skal være Herren helliget, det skal ikke samles til Liggendefæ, ej heller henlægges; thi de, som bo for Herrens Ansigt, skulle have dens Købmandsskab, at de maa æde og blive mætte og kunne klæde sig herligt.