< Ishaya 22 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
Detta är tungen öfver synedalen: Hvad är eder, att I så alle löpen på taken?
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
Du vast full med gny, en stad full med folk, en glad stad; dine slagne äro icke med svärd slagne, och icke döde blefne i strid;
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
Utan alle dine höfvitsmän äro tillika bortvekne för båga, och fångne; alle de, Som man uti dig funnit hafver, äro fångne, och långt bortflydde.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
Derföre säger jag: Går ifrå mig, låter mig bitterliga gråta; farer icke efter att hugsvala mig öfver mins folks dotters förstöring.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
Ty det är en bullers, förtryckelses och bekymmers dag af Herranom Zebaoth, i synedalenom, för murarnas undergrafnings skull, och för ropets skull på berget.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
Ty Elam drager med koger, vagnar, folk och resenärar, och Kir glimmar af sköldar.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
Och skall ske, att dina utkorade dalar skola med vagnar fulle varda, och resenärer skola lägga sig för portarna.
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
Då skall Juda förlåt öppnad varda, att man skall kunna se, på den tiden, tygen uti skogshuset.
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
Och I skolen se refvorna många vara på Davids stad, och skolen församla vatten uti dem nedra dammenom.
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
I skolen ock räkna, husen i Jerusalem, ja, I skolen afbryta husen, till att befästa murarna.
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
Och I skolen göra ena vattugraf, emellan båda murarna af den gamla dammens vatten; likväl sen I icke uppå den som detta gör, och skåden icke på den som sådant beställt hafver fjerranefter.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
Derföre skall Herren, Herren Zebaoth på den tiden låta utropa, att man skall gråta och jämra sig, och kulla sig, och draga säck uppå;
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
Ändock nu, si; intet annat är än glädje, slagta oxar, dräpa får, äta kött, dricka vin, och säga: Låt oss äta och dricka, vi måste dock i morgon dö.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
Detta är för Herrans Zebaoths öron uppenbart. Hvad gäller, om eder denna missgerningen förlåtas skall, tilldess I dön, säger Herren, Herren Zebaoth.
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
Så säger Herren, Herren Zebaoth: Gack in till räntomästaren Sebna, hofmästaren, och säg till honom:
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
Hvad hafver du här? Hvem hörer du till? att du låter dig hugga en graf, såsom den der låter sig hugga en graf i höjdene, och såsom den der låter sig göra en boning i bergklippone?
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
Si, Herren skall förkasta dig, såsom en stark man någon bortkastar, och nederkrafsa dig;
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
Och skall omdrifva dig, såsom ett klot på vida mark; der skall du dö, der skola dina kosteliga vagnar blifva med dins herras hus försmädelse.
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
Och jag skall störta dig ifrå ditt stånd, och sätta dig af ditt ämbete.
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
Och på den tiden vill jag kalla min tjenare Eliakim, Hilkia son;
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
Och draga din kjortel uppå honom, och omgjorda honom med ditt bälte, och gifva ditt välde uti hans hand, att han skall vara deras fader, som i Jerusalem och Juda hus bo;
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
Och skall lägga Davids hus nyckel uppå hans axlar, att han skall upplåta, och ingen skall tillsluta; att han skall tillsluta, och ingen upplåta.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
Och jag vill inslå honom för en nagla på ett fast rum, och han skall hafva ärones stol uti sins faders hus;
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
Att man skall hänga uppå honom all hans faders hus härlighet, barn och barnabarn, all små tyg, både dryckekar och allahanda strängaspel.
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
På den tiden, säger Herren Zebaoth, skall nagelen borttagen varda, den på det fasta rummet står, så att han skall söndergå och falla, och hans börda förgås; ty Herren säger det.

< Ishaya 22 >