< Ishaya 22 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
Breme dolini viðenja. Što ti je te si sva izašla na krovove?
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
Grade puni vike i vreve, grade veseli! tvoji pobijeni nijesu pobijeni maèem niti pogiboše u boju.
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
Glavari tvoji uzmakoše svikoliki, povezaše ih strijelci; što se god naðe tvojih, svi su povezani, ako i pobjegoše daleko.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
Zato rekoh: proðite me se, da plaèem gorko; ne trudite se da me tješite za pogiblju kæeri naroda mojega.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
Jer je ovo dan muke i potiranja i smetnje od Gospoda, Gospoda nad vojskama, u dolini viðenja; obaliæe zid, i vika æe biti do gore.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
I Elam uze tul, s kolima ljudi i s konjicima, i Kir istaèe štit.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
I krasne doline tvoje napuniše se kola, i konjici se namjestiše pred vratima.
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
I odastrije se zastiraè Judin; i pogledao si u to vrijeme na oružje u kuæi šumskoj.
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
I vidjeste da je mnogo proloma na gradu Davidovu, i sabraste vodu u donjem jezeru.
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
I izbrojiste kuæe Jerusalimske, i razvaliste kuæe da utvrdite zid.
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
I naèiniste jaz meðu dva zida za vodu iz staroga jezera; ali ne pogledaste na onoga koji je to uèinio i ne obazreste se na onoga koji je to odavna spremio.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
I zva vas Gospod nad vojskama u onaj dan da plaèete i ridate i da skubete kose i pripašete kostrijet;
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
A gle, radost i veselje, ubijaju goveda, kolju ovce, jedu meso i piju vino govoreæi: jedimo i pijmo, jer æemo sjutra umrijeti.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
Ali Gospod nad vojskama javi mi: neæe vam se oprostiti ovo bezakonje do smrti, veli Gospod, Gospod nad vojskama.
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
Ovako veli Gospod, Gospod nad vojskama: idi k onomu riznièaru, k Somni, upravitelju dvorskom,
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
I reci mu: šta æeš ti tu? i ko ti je tu? te si tu istesao sebi grob? istesao si sebi grob na visoku mjestu i spremio si sebi stan u kamenu.
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
Evo, èovjeèe, Gospod æe te baciti daleko i zatrpaæe te.
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
Zavitlaæe te i hititi kao loptu u zemlju prostranu; ondje æeš umrijeti i ondje æe biti kola slave tvoje, sramoto domu gospodara svojega;
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
I svræi æu te s mjesta tvojega, i istjeraæu te iz službe tvoje.
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
I u to vrijeme pozvaæu slugu svojega Elijakima sina Helkijina;
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
I obuæi æu mu tvoju haljinu, i tvojim æu ga pojasom opasati, i tvoju æu mu vlast dati u ruku, i biæe otac Jerusalimljanima i domu Judinu.
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
I metnuæu mu kljuè od doma Davidova na rame: kad on otvori, neæe niko zatvoriti, i kad on zatvori, neæe niko otvoriti.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
I kao klin uglaviæu ga na tvrdu mjestu, i biæe prijesto slave domu oca svojega;
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
I o njemu æe se vješati sva slava doma oca njegova, sinova i unuka, svakojaki sudovi, i najmanji, i èaše i mjehovi.
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
U to vrijeme, veli Gospod nad vojskama, pomjeriæe se klin uglavljeni na tvrdom mjestu, i izvadiæe se i pašæe, i teža što je na njemu propašæe; jer Gospod reèe.

< Ishaya 22 >