< Ishaya 22 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
وحی درباره وادی رویا: الان تو را چه شد که کلیه بر بامهابرآمدی؟۱
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
‌ای که پر از شورشها هستی و‌ای شهرپرغوغا و‌ای قریه مفتخر. کشتگانت کشته شمشیر نیستند و در جنگ هلاک نشده‌اند.۲
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
جمیع سرورانت با هم گریختند و بدون تیراندازان اسیر گشتند. همگانی که در تو یافت شدند با هم اسیر گردیدند و به‌جای دور فرارکردند.۳
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
بنابراین گفتم نظر خود را از من بگردانیدزیرا که با تلخی گریه می‌کنم. برای تسلی من درباره خرابی دختر قومم الحاح مکنید.۴
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
زیرا خداوند یهوه صبایوت روز آشفتگی وپایمالی و پریشانی‌ای در وادی رویا دارد. دیوارها را منهدم می‌سازند و صدای استغاثه تا به کوهها می‌رسد.۵
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
و عیلام با افواج مردان و سواران ترکش را برداشته است و قیر سپر را مکشوف نموده است،۶
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
و وادیهای بهترینت از ارابه‌ها پرشده، سواران پیش دروازه هایت صف آرایی می‌نمایند،۷
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
و پوشش یهودا برداشته می‌شود ودر آن روز به اسلحه خانه جنگل نگاه خواهیدکرد.۸
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
و رخنه های شهر داود را که بسیارندخواهید دید و آب برکه تحتانی را جمع خواهیدنمود.۹
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
و خانه های اورشلیم را خواهید شمرد وخانه‌ها را به جهت حصاربندی دیوارها خراب خواهید نمود.۱۰
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
و درمیان دو دیوار حوضی برای آب برکه قدیم خواهید ساخت اما به صانع آن نخواهید نگریست و به آنکه آن را از ایام پیشین ساخته است نگران نخواهید شد.۱۱
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
و در آن روزخداوند یهوه صبایوت (شما را) به گریستن و ماتم کردن و کندن مو و پوشیدن پلاس خواهدخواند.۱۲
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
و اینک شادمانی و خوشی و کشتن گاوان و ذبح کردن گوسفندان و خوردن گوشت ونوشیدن شراب خواهد بود که بخوریم و بنوشیم زیرا که فردا می‌میریم.۱۳
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
و یهوه صبایوت درگوش من اعلام کرده است که این گناه شما تابمیرید هرگز کفاره نخواهد شد. خداوند یهوه صبایوت این را گفته است.۱۴
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
خداوند یهوه صبایوت چنین می‌گوید: «برو و نزد این خزانه‌دار یعنی شبنا که ناظر خانه است داخل شو و به او بگو:۱۵
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
تو را در اینجا چه‌کار است و در اینجا که را داری که در اینجا قبری برای خود کنده‌ای؟ ای کسی‌که قبر خود را درمکان بلند می‌کنی و مسکنی برای خویشتن درصخره می‌تراشی.»۱۶
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
اینک‌ای مرد، خداوند البته تو را دورخواهد انداخت و البته تو را خواهد پوشانید.۱۷
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
والبته تو را مثل گوی سخت خواهد پیچید و به زمین وسیع تو را خواهد افکند و در آنجا خواهی مرد و در آنجا ارابه های شوکت تو رسوایی خانه آقایت خواهد شد.۱۸
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
و تو را از منصبت خواهم راند و از مکانت به زیر افکنده خواهی شد.۱۹
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
و در آن روز واقع خواهد شد که بنده خویش الیاقیم بن حلقیا را دعوت خواهم نمود.۲۰
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
و او را به‌جامه تو ملبس ساخته به کمربندت محکم خواهم ساخت و اقتدار تو را به‌دست اوخواهم داد و او ساکنان اورشلیم و خاندان یهودارا پدر خواهد بود.۲۱
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
و کلید خانه داود را بر دوش وی خواهم نهاد و چون بگشاید احدی نخواهدبست و چون ببندد، احدی نخواهد گشاد.۲۲
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
و او را در جای محکم مثل میخ خواهم دوخت و برای خاندان پدر خود کرسی جلال خواهد بود.۲۳
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
وتمامی جلال خاندان پدرش را از اولاد و احفاد وهمه ظروف کوچک را از ظروف کاسه‌ها تا ظروف تنگها بر او خواهند آویخت.۲۴
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
و یهوه صبایوت می‌گوید که در آن روز آن میخی که در مکان محکم دوخته شده متحرک خواهد گردید و قطع شده، خواهد افتاد و باری که بر آن است، تلف خواهد شد زیرا خداوند این راگفته است.۲۵

< Ishaya 22 >