< Ishaya 22 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
La charge de la vallée de vision. Qu'as-tu maintenant, que tu sois toute montée sur les toits,
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
Toi pleine de tumulte, ville bruyante, ville qui ne demandais qu'à t'égayer? tes blessés à mort n'ont pas été blessés à mort par l'épée, et ils ne sont pas morts par la guerre.
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
Tous tes conducteurs sont allés errant çà et là ensemble, ils ont été liés par les archers; tous ceux des tiens qui ont été trouvés ont été liés ensemble, s'en étant fuis loin.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
C'est pourquoi j'ai dit; retirez-vous de moi, je pleurerai amèrement. Ne vous empressez point de me consoler touchant le dégât de la fille de mon peuple.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
Car c'est le jour de trouble, d'oppression, et de perplexité, de par le Seigneur, l'Eternel des armées, dans la vallée de vision; il s'en va démolir la muraille, et le cri en ira jusqu'à la montagne.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
Même Hélam a pris son carquois, [il y a] des hommes montés sur des chariots, et Kir a découvert le bouclier.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
Et il est arrivé que l'élite de tes vallées a été remplie de chariots, et les gens de cheval se sont tous rangés en bataille contre la porte.
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
Et on a découvert ce qui couvrait Juda, et tu as regardé en ce jour-là vers les armes de la maison du parc.
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
Et vous avez vu que les brèches de la cité de David étaient grandes; et vous avez assemblé les eaux du bas étang.
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
Et vous avez fait le dénombrement des maisons de Jérusalem, et démoli les maisons pour fortifier la muraille.
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
Vous avez aussi fait un réservoir d'eaux entre les deux murailles, pour les eaux du vieux étang; mais vous n'avez point regardé à celui qui l'a faite et formée dès longtemps.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
Et le Seigneur, l'Eternel des armées, [vous] a appelés ce jour-là aux pleurs et au deuil, à vous arracher les cheveux, et à ceindre le sac;
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
Et voici il y a de la joie et de l'allégresse; on tue des bœufs, on égorge des moutons, on en mange la chair, et on boit du vin; [puis on dit]; Mangeons et buvons; car demain nous mourrons.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
Or l'Eternel des armées m'a déclaré, disant; si jamais cette iniquité vous est pardonnée, que vous n'en mouriez, a dit le Seigneur, l'Eternel des armées.
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
Ainsi a dit le Seigneur, l'Eternel des armées; va, entre chez ce trésorier, chez Sebna maître d'hôtel [et lui dis];
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
Qu'as-tu à faire ici? et qui [est] ici qui t'appartienne, que tu te sois taillé ici un sépulcre? Il taille un lieu éminent pour son sépulcre, et se creuse une demeure dans un rocher.
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
Voici, ô homme! l'Eternel te chassera loin, et te couvrira entièrement.
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
Il te fera rouler fort vite comme une boule en un pays large et spacieux; tu mourras là, et là seront les chariots de ta gloire, [de toi qui es] la honte de la maison de ton Seigneur.
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
Et je te jetterai hors de ton rang, et on te déposera de ton emploi.
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
Et il arrivera en ce jour-là que j'appellerai mon serviteur Eliakim, fils de Hilkija.
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
Et je le vêtirai de ta casaque, je le ceindrai de ton baudrier, je mettrai ton autorité entre ses mains, et il sera pour père à ceux qui habitent dans Jérusalem, et à la maison de Juda.
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
Et je mettrai la clef de la maison de David sur son épaule; et il ouvrira, et il n'y aura personne qui ferme; et il fermera, et il n'y aura personne qui ouvre.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
Et je le ficherai comme un croc en un lieu ferme; et il sera pour trône de gloire à la maison de son père.
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
Et on y pendra toute la gloire de la maison de son père, de ses parents, et de celles qui lui appartiennent; tous les ustensiles des plus petites choses, depuis les ustensiles des tasses jusques à tous les ustensiles des musettes.
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
En ce jour-là, dit l'Eternel des armées, le croc qui avait été fiché en un lieu ferme, sera ôté; et étant retranché il tombera, et ce dont il était chargé sera retranché; car l'Eternel a parlé.

< Ishaya 22 >