< Ishaya 22 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
Oracle contre la vallée de la Vision: "Qu’as-tu donc à monter tout entière sur les toits,
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
ô ville pleine de rumeurs, tumultueuse cité, toujours si joyeuse? Tes morts n’ont pas péri par le glaive, n’ont pas succombé dans les combats.
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
Tes chefs qui s’enfuient de concert sont pris sans être frappés par l’arc; ceux des tiens qui sont atteints sont capturés tous à la fois, tandis qu’ils se sauvent au loin.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
Aussi j’ai dit: "Laissez-moi, je veux répandre des larmes amères, ne vous mettez pas en peine pour me consoler du désastre de la fille de mon peuple.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
Car c’est un jour de trouble, de ruine et d’effarement qu’a décrété le Seigneur, Dieu-Cebaot, contre la vallée de la Vision: on abat les murailles et des cris résonnent dans les montagnes.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
Elam saisit le carquois, soutenu par des chars pleins de combattants et par des cavaliers, et Kir a mis à découvert son bouclier.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
Tes plus belles vallées sont envahies par des chars, et les cavaliers sont rangés près des portes.
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
Et quand l’ennemi a enlevé ainsi le voile de Juda, tu mets alors ton espoir dans l’arsenal de la Maison de la Forêt.
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
Vous constatez les nombreuses brèches de la ville de David et emmagasinez les eaux de la Piscine inférieure.
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
Vous faites le recensement des maisons de Jérusalem, et abattez des maisons pour fortifier les remparts.
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
Vous établissez un réservoir entre les deux murs pour les eaux de la vieille Piscine; mais vous n’avez pas de regard pour Celui qui est cause de tout cela, et vous ne savez pas reconnaître Celui qui l’a préparé de loin.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
En ce jour, ce à quoi vous invite le Seigneur, Dieu-Cebaot, c’est à pleurer, à vous lamenter, à vous raser la tête, à ceindre le cilice.
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
Or, voilà que chez vous tout est plaisir, allégresse, tuerie de bœufs, égorgement de moutons, mangerie de viandes, beuverie de vin: "Mangeons et buvons, dites-vous, car demain nous mourrons."
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
Mais l’arrêt de l’Eternel-Cebaot a été révélé à mes oreilles: "Ah! je le jure, ce péché ne vous sera point pardonné, jusqu’à votre mort," telle est la déclaration du Seigneur, Dieu-Cebaot.
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
Ainsi parla le Seigneur, Dieu-Cebaot: "Va, transporte-toi auprès de ce haut dignitaire, auprès de Chebna, intendant du palais pour lui dire:
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
Que possèdes-tu à toi en ces lieux, qui t’appartient ici, pour t’y creuser un sépulcre? II ose se creuser un sépulcre sur les hauteurs, se tailler une demeure dans le roc!
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
Voici, l’Eternel va t’empoigner avec vigueur, te faire tourner sur toi-même;
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
il te roulera comme une pelote, te lancera comme une boule vers un pays aux vastes espaces. Là, tu mourras, là iront tes chars somptueux, ô toi, honte de la maison de ton maître.
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
Ainsi je te précipiterai de ton poste et te culbuterai de ta place."
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
En ce jour, je ferai appel à mon serviteur Eliakim, fils de Hilkyyâhou.
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
Je le revêtirai de ta tunique, fixerai autour de lui ta ceinture et remettrai ton pouvoir entre ses mains; il sera un père pour les habitants de Jérusalem et la maison de Juda.
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
Je poserai la clef de la maison de David sur son épaule: il ouvrira et personne ne fermera, il fermera et personne n’ouvrira.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
Je le planterai solidement comme un clou dans un mur résistant, et il deviendra un trône de gloire pour la maison de son père.
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
Tout l’honneur de la maison de son père sera suspendu à lui les rejetons directs comme les branches éloignées, les plus petits ustensiles, depuis les bassins de métal jusqu’aux vases d’argile.
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
En ce jour, dit l’Eternel-Cebaot, le clou planté dans un endroit solide cédera, il sera abattu et tombera, et avec lui sera ruinée toute la charge qu’il supporte. C’Est l’Eternel qui a parlé.

< Ishaya 22 >