< Ishaya 22 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
[I received] this message [from Yahweh] about Jerusalem, about the valley where [Yahweh showed me] this vision. Why is everyone foolishly running up to their [flat] rooftops?
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
Everyone in the city [seems to] be shouting. [There are a lot of] corpses [in the city], [but they] were not killed by [their enemies’] swords. They did not die in battles; [instead, they died from diseases and hunger].
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
All the leaders of the city fled. [But then] they were captured because they did not have bows [and arrows to defend themselves]. Your [soldiers tried to] flee while the enemy [army] was still far away, but they also were captured.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
That is why I said, “Allow me to cry alone; do not try to comfort me [about my people being slaughtered].”
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
The Commander of the armies of angels has [chosen] a time when there will be a great uproar, [soldiers] marching, and people being terrified in the valley [where I received this] vision. [It will be a time when our city] walls will be battered down and [the people’s] cries [for help] will be heard in the mountains.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
The armies from Elam and Kir [in Media] will attack, driving chariots and carrying shields.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
Our beautiful valleys will be filled with [our enemies’] chariots and the men who drive the chariots will stand outside [our city] gates.
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
The walls that protect [the cities in] Judah will fall down. You [people of Jerusalem] will run to get the weapons [that are stored in the building called] “the Hall of the Forest”.
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
You will see that there are many breaks/holes in the walls of Jerusalem. You will store water in the lower pool [in the city].
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
You will inspect the houses in Jerusalem, and [some of] them you will tear down to use the stones to repair the [city] wall.
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
Between the walls [of the city] you will build a reservoir to [store] water from the old pool. But you will never request help from the one who made the city; you have never depended on Yahweh, who planned this city long ago.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
The Commander of the armies of angels told you to weep and mourn; he told you to shave your heads and to wear rough sackcloth to show that you were sorry for the sins that you had committed.
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
But instead of doing that, you were happy and celebrating; you slaughtered cattle and sheep, [in order to cook their] meat and eat it and drink wine. You said, “Let’s eat and drink [all that we want to], because [it is possible that] we will die tomorrow!”
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
[So] the Commander of the armies of angels revealed this to me: “I will never forgive my people for sinning like this!”
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
The Commander of the armies of angels said this [to me]: “Go to Shebna, the official who supervises the workers in the palace, and give this message to him:
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
'[Who do you think you are?] Who gave you the authority to build a beautiful tomb where you will be buried, chiseling it out of the rocky cliff high above this valley?
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
You [think that you are] [IRO] a great man, but Yahweh is about to hurl you away. [It will be as though] he will seize you,
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
and roll/crumple you into a ball and throw you away into a large distant land. You will die [and be buried] there, and your beautiful chariots will stay there [in the hands of your enemies]. And [because of what happens to you], your master, [the king], will be [very] ashamed/disgraced.
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
Yahweh will force you to quit working in the palace; you will be demoted from your important position.
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
Then I will summon Hilkiah’s son Eliakim, who has served serve me [well], to replace you.
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
I will allow him to wear your robe, and to fasten your sash around him, and I will give to him the authority that you had. He will be like [MET] a father to the people of Jerusalem and [all the other] towns in Judah.
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
I will give to him authority [MTY] over [what happens in] the palace where King David [lived]; when he decides something [MET], no one will be able to oppose it; when he refuses to do something, no one will be able to force him to do it.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
I will cause his family to be greatly respected, because I will put him firmly in his position [as supervisor of the workers in the palace], like [SIM] a nail that is firmly hammered into a wall.
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
Others will enable him to have much responsibility, with the result that all the members of his family, even the most insignificant ones, will be honored.'”
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
[But] the Commander of the armies of angels also says, “[Shebna is like] [MET] a peg that is firmly fastened to the wall. But there will be a time when I will [remove him from his position]; he will lose his power/influence, and everything that he promoted [MET] will fail. [That will surely happen] because [I], Yahweh, have said it.”