< Ishaya 22 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
The prophecy concerning the valley of vision. What aileth thee now, That all thine inhabitants are gone up to the house-tops?
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
Thou that wast full of noise, A tumultuous city, a joyous city! Thy slain fall not by the sword; They are not slain in battle.
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
All thy leaders flee together, By the bowmen are they bound; All found within thee are made captive together, Even they who have fled from afar.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
Therefore, say I, look away from me, that I may weep bitterly; Strive not to comfort me for the desolation of the daughter of my people!
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
For a day of trouble, of desolation, and of perplexity cometh From the Lord, Jehovah of hosts, in the valley of vision. They break down the walls; The cry reacheth to the mountains.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
Elam beareth the quiver, With chariots full of men, and with horsemen; Kir uncovereth the shield.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
Thy fairest valleys, [[O Jerusalem, ]] are full of chariots; The horsemen set themselves in array against the gate;
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
The veil of Judah is torn from her. But in such a day ye look to the armor of the house of the forest;
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
Ye mark how many are the breaches of the city of David, And collect the waters of the lower pool;
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
Ye number the houses of Jerusalem, And ye break down the houses to prepare the wall;
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
Ye make a reservoir between the two walls for the waters of the old pool; But ye look not to Him who hath done this; Ye regard not Him that hath prepared this from afar.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
The Lord, Jehovah of hosts, calleth you this day To weeping and to lamentation, To baldness and to girding with sackcloth.
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
But, behold, joy and gladness, Slaying oxen and killing sheep, Eating flesh and drinking wine! “Let us eat and drink, For to-morrow we die!”
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
Therefore it hath been revealed in my ears by Jehovah of hosts; “This iniquity shall not be forgiven you, till ye die,” Saith the Lord, Jehovah of hosts.
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
Thus saith the Lord, Jehovah of hosts: Go in to this steward, To Shebna, who is over the household, and say,
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
What hast thou here, and whom hast thou here, That thou here hewest thee out a sepulchre, —That thou hewest out thy sepulchre on high, And gravest out a habitation for thyself in the rock?
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
Behold, Jehovah will cast thee headlong with a mighty thrust;
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
He will violently roll thee together like a ball; Like a ball will he hurl thee into a wide country. There shalt thou die; And there shall be thy splendid chariots, Thou disgrace of the house of thy lord!
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
I will drive thee from thy post, And from thy station I will pull thee down.
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
In that day I will call my servant, Even Eliakim, the son of Hilkiah;
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
I will clothe him with thy robe, And bind thy girdle around him; Thy government will I commit to his hand, And he shall be a father to the inhabitants of Jerusalem, And to the house of Judah.
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
I will lay the key of the house of David upon his shoulder; He shall open, and none shall shut, And he shall shut, and none shall open.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
I will fasten him as a peg in a sure place, And he shall be a glorious seat for his father's house.
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
Upon him shall hang all the glory of his father's house, The offspring and the offshoots; Every small vessel, from the goblet even to all the pitchers.
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
In that day, saith Jehovah of hosts, The peg that was once fastened in a sure place shall be moved; It shall be cut down, and fall, And the burden which was upon it shall come to the ground. For Jehovah hath said it.

< Ishaya 22 >