< Ishaya 22 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
The burden of the Valley of Vision. What is [troubling] you now, that you have gone up, All of you—to the roofs?
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
Full of stirs—a noisy city—an exulting city, Your pierced are not pierced of the sword, Nor dead in battle.
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
All your rulers fled from the bow together, All found of you have been bound, They have been kept bound together, They have fled far off.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
Therefore I said, “Look [away] from me, I am bitter in my weeping, do not hurry to comfort me, For the destruction of the daughter of my people.”
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
For a day of noise, and of treading down, And of perplexity, [is] to the Lord, YHWH of Hosts, In the Valley of Vision, digging down a wall, And crying to the mountain.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
And Elam has carried a quiver, In a chariot of men—horsemen, And Kir has exposed a shield.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
And it comes to pass, The choice of your valleys have been full of chariots, And the horsemen diligently place themselves at the gate.
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
And one removes the covering of Judah, And in that day you look To the armor of the house of the forest,
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
And you have seen the breaches of the City of David, For they have become many, And you gather the waters of the lower pool,
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
And you numbered the houses of Jerusalem, And you break down the houses to fortify the wall.
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
And you made a ditch between the two walls, For the waters of the old pool, And you have not looked to its Maker, And you have not seen its Framer of old.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
And the Lord calls, YHWH of Hosts, In that day, to weeping and to lamentation, And to baldness and to girding on of sackcloth,
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
And behold, joy and gladness, slaying of oxen, And slaughtering of sheep, Eating of flesh, and drinking of wine, Eat and drink, for tomorrow we die.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
And it has been revealed in my ears, [By] YHWH of Hosts: This iniquity is not pardoned to you, Until you die, said the Lord, YHWH of Hosts.
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
Thus said the Lord, YHWH of Hosts: “Go forth, go to this steward, To Shebna, who [is] over the house:
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
What are you [doing] here? And who has [allowed] you here? That you have hewn out a tomb for yourself here? Hewing his tomb on high, Carving a dwelling for himself in a rock.
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
Behold, YHWH is casting you up and down, A casting up and down, O mighty one,
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
And your coverer covering, wrapping around, Wraps you around, O babbler, On a land of broad sides—there you die, And there the chariots of your glory [are] the shame of the house of your lord.
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
And I have thrust you from your station, And he throws you down from your office.
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
And it has come to pass in that day, That I have called to My servant, To Eliakim son of Hilkiah.
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
And I have clothed him with your coat, And I strengthen him with your girdle, And I give your garment into his hand, And he has been for a father to the inhabitant of Jerusalem, And to the house of Judah.
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
And I have placed the key Of the house of David on his shoulder, And he has opened, and none is shutting, And has shut, and none is opening.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
And I have fixed him [as] a nail in a steadfast place, And he has been for a throne of glory To the house of his father.
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
And they have hanged on him All the glory of the house of his father, The offspring and the issue, All vessels of small quality, From vessels of basins to all vessels of flagons.
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
In that day—a declaration of YHWH of Hosts, The nail that is fixed is moved In a steadfast place, Indeed, it has been cut down, and has fallen, And the burden that [is] on it has been cut off, For YHWH has spoken!”