< Ishaya 22 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
The doom of the valley of vision. What aileth thee now, that thou art wholly gone up to the roofs?
2 Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
O noiseful, tumultuous city, joyous town? thy slain ones are not slain with the sword, and not those that die in battle.
3 Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
All thy rulers are fled together, they are made prisoners by the bowmen: all that are found in thee are made prisoners together, who have run away from afar.
4 Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
Therefore said I, Look away from me; I will weep bitterly; be not urgent to comfort me, because of the wasting of the daughter of my people.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
For a day of confusion, and of treading down, and of perplexity hath the Lord Eternal of hosts in the valley of vision; walls are broken, and crying is heard against the mountain.
6 Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
And 'Elam beareth the quiver, [cometh] with men in chariots and horsemen, and Kir uncovereth the shield.
7 Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
And it is so, that thy choicest valleys are full of chariots, and the horsemen set themselves in array against the gate.
8 An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
And he laid open the covering of Judah; and thou didst look on that day toward the armor of the house of the forest.
9 kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
And the breaches of the city of David have ye seen, that they are many: and ye gathered together the waters of the lower pool.
10 Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
And the houses of Jerusalem have ye numbered, and ye have pulled down the houses to fortify the wall.
11 Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
And a tank have ye made between the two walls for the water of the old pool; but ye have not looked at the Maker thereof, him that fashioned it in distant times have ye not regarded.
12 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
And the Lord Eternal of hosts called on that day for weeping, and for mourning, and for baldness, and for girding with sackcloth.
13 Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
And behold [there are] gladness and joy, slaying of oxen, and killing of sheep, eating flesh, and drinking wine: “Let us eat and drink; for tomorrow we must die.”
14 Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
And it was revealed in my ears by the Lord of hosts: Surely this iniquity shall not be forgiven unto you until ye die, said the Lord the Eternal of hosts.
15 Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
Thus hath said the Lord, Go, get thee unto this treasurer, even unto Shebna, who is [superintendent] over the house;
16 Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
What hast thou here? and whom hast thou here, that thou hast hewn out for thyself here a sepulchre, [the man] that hath hewn out on high his sepulchre, that holloweth out in the rock a habitation for himself?
17 “Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
Behold, the Lord will thrust thee about with a mighty throw, O man! and will lay fast hold of thee;
18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
He will roll thee up as a bundle, and [toss thee] like a ball into a country of ample space: there shalt thou die, and there shall [remain] the chariots of thy glory, thou disgrace of the house of thy lord.
19 Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
And I will cast thee out from thy station, and from thy post shall he pull thee down.
20 “A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
And it shall come to pass on that day, that I will call my servant, for Elyakim the son of Chilkiyahu.
21 Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
And I will clothe him with thy robe, and thy girdle will I fasten around him, and thy government will I place into his hand: and he shall be as a father to the inhabitants of Jerusalem, and to the house of Judah.
22 Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
And I will lay the key of the house of David upon his shoulder; so that he shall open, and none shall shut; and he shall shut, and none shall open.
23 Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
And I will fasten him as a tent-nail in a sure place; and he shall be for a chair of honor to his father's house.
24 Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
And they shall hang upon him all the glory of his father's house, the shoots and offshoots, all the small vessels, from the vessels of basins, even to all the vessels of flagons.
25 “A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
On that day, saith the Lord of hosts, shall be removed the nail that is fastened in the sure place, and be cut down, and fall; and the burden that is upon it shall be cut off; for the Lord hath spoken it.