< Ishaya 21 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
Utsaga om Öknen vid havet. Likasom en storm som far fram i Sydlandet kommer det från öknen, från det fruktansvärda landet.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
En gruvlig syn har blivit mig kungjord: "Härjare härja, rövare röva. Drag upp, du Elam! Träng på, du Mediens folk! På all suckan vill jag göra slut."
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Fördenskull darra nu mina länder, ångest griper mig, lik en barnaföderskas ångest; förvirring kommer över mig, så att jag icke kan höra, förskräckelse fattar mig, så att jag icke kan se.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
Mitt hjärta är utom sig, jag kväljes av förfäran; skymningen, som jag längtade efter, vållar mig nu skräck.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
Man dukar bord, man breder ut täcken, man äter och dricker. Nej, stån upp, I furstar; smörjen edra sköldar!
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
Ty så har Herren sagt till mig: "Gå och ställ ut en väktare; vad han får se, det må han förkunna.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
Och om han ser ett tåg, ryttare par efter par, ett tåg av åsnor, ett tåg av kameler, då må han giva akt, noga giva akt."
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
Och denne ropade, såsom ett lejon ryter: "Herre, här står jag på vakt beständigt, dagen igenom, och jag förbliver här på min post natt efter natt.
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Och se, nu kommer här ett tåg av män, ryttare par efter par!" Och åter talade han och sade: "Fallet, fallet är Babel! Alla dess gudabeläten äro nedbrutna till jorden."
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
O du mitt krossade, mitt söndertröskade folk, vad jag har hört av HERREN Sebaot, Israels Gud, det har jag förkunnat för eder.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
Utsaga om Duma. Man ropar till mig från Seir: "Väktare, vad lider natten? Väktare, vad lider natten?"
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
Väktaren svarar: "Morgon har kommit, och likväl är det natt. Viljen I fråga mer, så frågen; kommen tillbaka igen."
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
Utsaga över Arabien. Tagen natthärbärge i Arabiens vildmark, I karavaner från Dedan.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
Må man komma emot de törstande och giva dem vatten. Ja, inbyggarna i Temas land gå de flyktande till mötes med bröd.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
Ty de fly undan svärd, undan draget svärd, och undan spänd båge och undan krigets tunga.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
Ty så har Herren sagt till mig: Om ett år, såsom dagakarlen räknar året, skall all Kedars härlighet vara förgången,
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
och föga skall då vara kvar av Kedars hjältars bågar, så många de äro. Ty så har HERREN, Israels Gud, talat.