< Ishaya 21 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
Бреме пустињи на мору. Као вихори који пролазе на југ, тако ће доћи из пустиње, из земље страшне.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
Љута утвара јави ми се. Неверник неверу чини, пустошник пустоши; ходи, Еламе; опколи, Мидијо! Свему уздисању учинићу крај.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Зато су бедра моја пуна бола; муке ме обузеше као кад се мучи породиља; згурих се чујући, препадох се видећи.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
Срце ми се смете, гроза ме подузе; ноћ милина мојих претвори ми се у страх.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
Постави сто, стражар нека стражи; једи, пиј; устајте кнезови, мажите штитове.
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
Јер овако ми рече Господ: Иди, постави стражара да ти јави шта види.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
И виде кола, и два реда коњика; кола с магарцима и кола с камилама; и пажаше добро великом пажњом.
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
И повика као лав: Господару, ја стојим једнако на стражи дању, и стојим на стражи по сву ноћ.
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
И ево дођоше на колима људи, у два реда коњици. Тада повика и рече: Паде, паде Вавилон, и сви резани ликови богова његових разбише се о земљу.
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
Вршају мој, и пшенице гумна мог! Шта чух од Господа над војскама, Бога Израиљевог, јавих вам.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
Бреме Думи. Виче к мени неко са Сира: Стражару! Шта би ноћас? Стражару! Шта би ноћас?
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
Стражар рече: Доћи ће јутро, али и ноћ; ако ћете тражити, тражите, вратите се, дођите.
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
Бреме арапској. По шумама у арапској ноћиваћете, путници дедански!
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
Изнесите воде пред жедне, који живите у земљи Теми, сретните с хлебом бегунца.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
Јер ће бежати од мача, од мача голог, од лука запетог и од жестоког боја.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
Јер овако ми рече Господ: За годину, као што је година најамничка, нестаће све славе кидарске.
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
И што остане храбрих стрелаца синова кидарских, биће мало; јер Господ Бог Израиљев рече.