< Ishaya 21 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
Prophétie sur le désert de la mer. Pareil aux ouragans du midi quand ils passent, il vient du désert, du pays redoutable.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
Une vision terrible m'a été révélée. Le perfide agit avec perfidie, et le dévastateur dévaste. Élamites, montez! Mèdes, assiégez! Je fais cesser tous ses gémissements!
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
C'est pourquoi mes reins sont remplis de douleur; des angoisses m'ont saisi, comme les angoisses de celle qui enfante; les douleurs m'empêchent d'entendre, l'épouvante m'empêche de voir!
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
Mon cœur est troublé; la terreur me saisit; la nuit de mes plaisirs est changée en nuit d'épouvante.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
On dresse la table; la sentinelle veille; on mange, on boit. Levez-vous, capitaines! Huilez le bouclier!
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
Car ainsi m'a dit le Seigneur: Va, place la sentinelle; qu'elle annonce ce qu'elle verra.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
Elle voit de la cavalerie, des cavaliers à cheval, deux à deux; des cavaliers sur des ânes, des cavaliers sur des chameaux; elle observe avec attention, avec grande attention.
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
Puis elle s'écrie, comme un lion: Seigneur, je me tenais en sentinelle sur la tour toute la journée, j'étais debout à mon poste toute la nuit;
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Et voici venir de la cavalerie, des cavaliers deux à deux! Elle prend encore la parole, et dit: Elle est tombée, elle est tombée, Babylone! Et toutes les images de ses dieux sont brisées par terre!
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
O mon peuple, froment battu, foulé dans mon aire! ce que j'ai entendu de la part de l'Éternel des armées, Dieu d'Israël, je vous l'ai annoncé.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
Prophétie sur Duma. On me crie de Séir: Sentinelle, qu'en est-il de la nuit? Sentinelle, qu'en est-il de la nuit?
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
La sentinelle dit: Le matin vient, et la nuit aussi. Si vous voulez interroger, interrogez; revenez encore.
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
Prophétie sur l'Arabie. Vous passerez la nuit dans les bois, en Arabie, troupes errantes de Dédan.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
Venez apporter de l'eau à ceux qui ont soif, habitants du pays de Théma. Venez au-devant du fugitif avec son pain.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
Car ils s'enfuient devant les épées, devant l'épée nue, devant l'arc tendu, devant le fort de la bataille.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
Car ainsi m'a dit le Seigneur: Encore une année comme les années d'un mercenaire, et toute la gloire de Kédar prendra fin;
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
Et le nombre des vaillants archers, fils de Kédar, sera réduit à un faible reste. Car l'Éternel, le Dieu d'Israël, a parlé.

< Ishaya 21 >