< Ishaya 21 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
Oracle contre la steppe enveloppée par la mer Prompt: comme les ouragans qui traversent le Midi, il vient du désert, d’une région terrible.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
Une vision effrayante m’a été révélée: "L’Oppresseur opprime, le ravageur ravage. Alerte, Elam, à l’assaut, Mèdes! Je vais mettre fin aux soupirs.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Voilà pourquoi mes reins sont saisis de tremblement, les douleurs m’ont envahi comme les douleurs d’une femme qui enfante. Je suis pris de vertige au point de ne plus entendre, terrifié au point de ne plus voir.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
Mon esprit s’égare, la frayeur m’a terrassé; la nuit qui m’était si chère s’est changée pour moi en épouvante.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
On dresse la table, on étend les tapis, on mange, on boit. "Debout, princes, huilez le bouclier!"
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
Voici, en effet, ce que m’a dit le Seigneur: "Va, place le guetteur à son poste, qu’il annonce ce qu’il verra!"
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
II verra une file de cavaliers, des chars conduits par des coursiers, des hommes montés à dos d’ânes, des hommes montés à dos de chameaux; puis il percevra une rumeur, une formidable rumeur.
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
Et il s’écriera avec la force du lion: "Sur la tour, Seigneur, je me tiens constamment le jour, et toutes les nuits je suis à mon poste."
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Et voici qu’arrivent des hommes à cheval, des chars traînés par des coursiers. De nouveau, élevant la voix, il dit: "Tombée, elle est tombée Babylone, toutes les idoles de ses divinités gisent à terre, réduites en pièces!
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
Ah! ma paille triturée, ô fils de mon aire! Ce que j’ai appris de la part de l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël, je vous l’annonce.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
Oracle contre Douma: Une voix crie vers moi de Séir: "Guetteur, où en est la nuit? Qu’en est-il de la nuit, guetteur?"
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
Le guetteur répond: "Le matin vient, puis ensuite la nuit. Si vous voulez des nouvelles, interrogez; refaites le même chemin, venez."
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
Oracle contre l’Arabie: Dans les forêts de l’Arabie, passez la nuit, caravanes de Dedân.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
Vous, habitants du pays de Têma, portez de l’eau au-devant de ceux qui ont soif, présentez aux fugitifs le pain qu’ils réclament.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
C’Est devant les glaives qu’ils ont fui, devant les glaives tranchants, devant les arcs tendus et devant la violence des combats.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
Voici, en effet, ce que m’a dit le Seigneur: "Encore une année, pareille aux années du travailleur salarié, et c’en sera fait de toute l’opulence de Kédar;
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
et les survivants des nombreux archers, des guerriers, enfants de Kêdar, seront réduits à peu de chose." C’Est l’Eternel, Dieu d’Israël, qui l’a proclamé.

< Ishaya 21 >