< Ishaya 21 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
L’oracle touchant le désert de la mer. Comme des tourbillons dans le midi quand ils passent, il vient du désert, du pays terrible.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
Une cruelle vision m’est révélée: Le perfide agit perfidement, et le destructeur détruit. Monte, Élam! assiège, Médie! J’ai fait cesser tout son gémissement.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
C’est pourquoi mes reins sont remplis de douleur; des angoisses m’ont saisi comme les angoisses de celle qui enfante; je suis courbé, à ne pas entendre; je suis terrifié, à n’y pas voir;
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
mon cœur bat; le tremblement s’est emparé de moi; la nuit de mon plaisir, il me l’a changée en effroi.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
Dresse la table; fais le guet; mange, bois… Princes, levez-vous, oignez le bouclier!
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
Car ainsi m’a dit le Seigneur: Va, place une sentinelle; qu’elle déclare ce qu’elle voit.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
Et elle vit un char, une paire de cavaliers, un char [attelé] d’ânes, un char [attelé] de chameaux. Et elle écouta diligemment, avec grande attention;
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
et elle cria [comme] un lion: Seigneur, je me tiens dans le poste d’observation constamment, de jour, et je suis là faisant ma garde toutes les nuits…
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Et voici, il vient un char d’hommes, une paire de cavaliers! Et il répondit, et dit: Babylone est tombée, elle est tombée, et toutes les images de ses dieux sont brisées par terre.
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
Ô vous, mon blé battu, et le fruit de mon aire! ce que j’ai entendu de l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël, je vous l’ai rapporté.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
L’oracle touchant Duma. Il me crie de Séhir: Sentinelle, à quoi en est la nuit? Sentinelle, à quoi en est la nuit?
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
La sentinelle dit: Le matin vient, et aussi la nuit. Si vous voulez vous enquérir, enquérez-vous; revenez, venez.
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
L’oracle contre l’Arabie. Vous logerez dans la forêt de l’Arabie, caravanes des Dedanites.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
À la rencontre de celui qui a soif apportez de l’eau! Les habitants du pays de Théma viennent avec leur pain au-devant de celui qui fuit;
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
car ils s’enfuient devant les épées, devant l’épée dégainée, et devant l’arc tendu, et devant le poids de la guerre.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
Car ainsi m’a dit le Seigneur: Encore une année comme les années d’un mercenaire, et toute la gloire de Kédar aura pris fin,
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
et le reste du nombre des archers des hommes forts des fils de Kédar sera amoindri; car l’Éternel, le Dieu d’Israël, a parlé.