< Ishaya 21 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
Oracle sur le désert de la mer. Comme les ouragans passent dans le midi, cela vient du désert, d’une terre redoutable.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
Une vision terrible m’a été montrée: le pillard pille et le ravageur ravage! Monte, Élam! Assiège, Mède! Je fais cesser tous les gémissements.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
C’est pourquoi mes reins sont remplis d’angoisses; des douleurs me saisissent, comme les douleurs d’une femme qui enfante. Je me tords à entendre, je m’épouvante à voir;
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
mon cœur s’égare, l’effroi me saisit; de la nuit que je désirais on a fait pour moi un temps de terreurs.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
On dresse la table, la sentinelle fait le guet, on mange, on boit. — « Debout, capitaines! Oignez le bouclier! »
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
Car ainsi m’a parlé le Seigneur: « Va, établis une sentinelle; qu’elle annonce ce qu’elle verra.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
Et elle verra des cavaliers, deux à deux, sur des chevaux, des cavaliers sur des ânes, des cavaliers sur des chameaux. Et elle regardera avec attention, avec grande attention. »
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
Et elle a crié comme un lion: « Sur la tour du guet, Seigneur, je me tiens, sans cesse tout le jour, et à mon poste je suis debout toutes les nuits.
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Voici qu’arrive de la cavalerie; des cavaliers deux à deux. » Et elle a repris et dit: « Elle est tombée, elle est tombée, Babylone, et toutes les statues de ses dieux, il les a brisées contre terre! »
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
Ô mon froment qu’on foule, grain de mon aire, ce que j’ai entendu de Yahweh des armées, du Dieu d’Israël, je vous l’annonce.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
Oracle sur Duma. On me crie de Séir: « Sentinelle, où en est la nuit? Sentinelle, où en est la nuit? »
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
La sentinelle répond: « Le matin vient et la nuit aussi. Si vous voulez m’interroger, interrogez; revenez une autre fois! »
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
Oracle en Arabie. Vous passerez la nuit dans les steppes en Arabie, caravanes de Dédan. —
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
À la rencontre de celui qui a soif, apportez de l’eau! Les habitant du pays de Théma offrent du pain aux fugitifs.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
Car ils ont fui devant l’épée, devant l’épée nue, devant l’arc bandé, devant la terrible bataille.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
Car ainsi m’a parlé le Seigneur: Encore une année, comptée comme les années du mercenaire, et c’en est fait de toute la gloire de Cédar;
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
et des arcs nombreux des vaillants fils de Cédar il ne restera que peu de chose; car Yahweh, le Dieu d’Israël, a parlé.

< Ishaya 21 >