< Ishaya 21 >
1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
The birthun of the forsakun see. As whirlewyndis comen fro the southwest, it cometh fro desert, fro the orible lond.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
An hard reuelacioun is teld to me; he that is vnfeithful, doith vnfeithfuli; and he that is a distriere, distrieth. Thou Helam, stie, and thou, Meda, biseche; Y made al the weilyng therof for to ceesse.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Therfor my leendis ben fillid with sorewe; angwische weldide me, as the angwisch of a womman trauelynge of child; Y felle doun, whanne Y herde; Y was disturblid, whanne Y siy.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
Myn herte fadide, derknessis astonieden me; Babiloyne, my derlyng, is set to me in to myracle.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
Sette thou a boord, biholde thou in to a toting place; rise, ye princes, etynge and drynkynge, take ye scheeld.
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
For whi the Lord seide these thingis to me, Go thou, and sette a lokere; and telle he, what euer thing he seeth.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
And he siy the chare of tweyne horse men, the stiere of an asse, and the stiere of a camel; and he bihelde diligentli with myche lokyng,
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
and criede as a lioun, Y stonde contynueli bi dai on the totyng place of the Lord, and Y stonde bi alle nyytis on my kepyng.
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Lo! this cometh, a man stiere of a carte of horse men. And Isaie criede, and seide, Babiloyne felle doun, felle doun; and alle the grauun ymagis of goddis therof ben al to-brokun in to erthe.
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
Mi threschyng, and the douyter of my cornfloor, Y haue teld to you what thingis Y herde of the Lord of oostis, of God of Israel.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
The birthun of Duma. It crieth fro Seir to me, Kepere, what our of the niyt? `kepere, what our of the niyt?
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
The kepere seide, Morewtid cometh, and niyt; if ye seken, seke ye, and be ye conuertid, and `come ye.
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
The birthun in Arabie. In the forest at euentid ye schulen slepe, in the pathis of Dodanym.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
Ye that dwellen in the lond of the south, renne, and bere watir to the thristi; and renne ye with looues to hym that fleeth.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
For thei fledden fro the face of swerdis, fro the face of swerd neiyynge, fro the face of bouwe bent, fro the face of greuouse batel.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
For the Lord seith these thingis to me, Yit in o yeer, as in the yeer of an hirid man, and al the glorie of Cedar schal be takun awei.
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
And the remenauntis of the noumbre of stronge archeris of the sones of Cedar schulen be maad lesse; for whi the Lord God of Israel spak.