< Ishaya 21 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
The oracle on the desert of the sea: As storm-winds in the South which with a rush from the desert, do come from a terrible land,
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
[So] hath, a grievous vision, been told me: —the deceiver, is deceiving. And the spoiler, is spoiling, Go up, O Elam Besiege O Media, All the sighing she hath caused, have I made to cease.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
For this cause, are my loins filled with anguish, Pangs, have seized me, as the pangs of her that is giving birth, —I writhe so that I cannot hear, I tremble, so that I cannot see:
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
My heart fluttereth, A horror, terrifieth me, —My twilight of pleasure, hath he turned for me into a time of trembling.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
[Ye thought] to prepare the table—spread the mat—eat—drink! …Arise ye chieftains anoint the shield!
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
For, thus, hath My Lord said unto me, —Go, set the watchman, What he seeth, let him tell!
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
When he seeth A train of horsemen in double rank, A train of asses, A train of camels, Then shall he hearken attentively with diligent heed.
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
Then cried he. A lion! On the watch, O My Lord, had I been standing continually, by day, And at my post, had I been stationed whole nights; —
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
When lo! here was a train of men coming. With horsemen in double rank, —And one began and said, Fallen! fallen! is Babylon, And all the images of her gods, are smashed to the ground!
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
O thou My threshing! And the grain of my corn-floor! That which I have heard from Yahweh of hosts, the God of Israel, Have I declared, unto you.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
The oracle on Dumah: Unto me, is one crying—out of Seir, Watchman! how far gone is the night? Watchman, how far gone is the night?
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
Said the watchman, There cometh a morning. But also a night, —If ye will enquire, enquire, ye—Come, again!
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
The oracle on Arabia, —Among the shrubs in Arabia, must ye lodge, Ye caravans of Dedanites.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
To meet the thirsty, bring ye water, —Ye dwellers in the land of Tema; With bread for him, get in advance of him that is in flight!
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
For, before swords, have they fled: Before a sword that is drawn, Before a bow that is bent, And before the stress of war.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
For, thus, hath My Lord said unto me, —Within a year according to the yearn of a hireling, shall fail all the glory of Kedar;
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
And, the remnant of the record of bowmen, The heroes of the sons of Kedar, shall become few; For Yahweh God of Israel, hath spoken.

< Ishaya 21 >