< Ishaya 21 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
The burden of the desert Sea. As the whirlewindes in the South vse to passe from the wildernesse, so shall it come from the horrible land.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
A grieuous vision was shewed vnto me, The transgressour against a transgressour, and the destroyer against a destroyer. Goe vp Elam, besiege Media: I haue caused all the mourning thereof to cease.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Therefore are my loynes filled with sorow: sorowes haue taken me as the sorowes of a woman that trauayleth: I was bowed downe when I heard it, and I was amased when I sawe it.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
Mine heart failed: fearefulnesse troubled me: the night of my pleasures hath he turned into feare vnto me.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
Prepare thou the table: watch in the watch towre: eate, drinke: arise, ye princes, anoynt the shielde.
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
For thus hath the Lord said vnto me, Go, set a watchman, to tell what he seeth.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
And he sawe a charet with two horsemen: a charet of an asse, and a charet of a camel: and he hearkened and tooke diligent heede.
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
And he cryed, A lyon: my lorde, I stand continually vpon ye watche towre in the day time, and I am set in my watche euery night:
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
And beholde, this mans charet commeth with two horsemen. And he answered and said, Babel is fallen: it is fallen, and all the images of her gods hath he broken vnto the ground.
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
O my threshing, and the corne of my floore. That which I haue heard of the Lord of hostes, the God of Israel, haue I shewed vnto you.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
The burden of Dumah. He calleth vnto me out of Seir, Watchman, what was in ye night? Watchman, what was in the night?
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
The watchman saide, The morning commeth, and also the night. If yee will aske, enquire: returne and come.
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
The burden against Arabia. In the forest of Arabia shall yee tarie all night, euen in the waies of Dedanim.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
O inhabitants of the lande of Tema, bring foorth water to meete the thirstie, and preuent him that fleeth with his bread.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
For they flee from the drawen swords, euen from the drawen sword, and from the bent bowe, and from the grieuousnesse of warre.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
For thus hath the Lord sayd vnto me, Yet a yeere according to the yeeres of an hireling, and all the glorie of Kedar shall faile.
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
And the residue of the nomber of ye strong archers of the sonnes of Kedar shall be fewe: for the Lord God of Israel hath spoken it.

< Ishaya 21 >