< Ishaya 20 >

1 A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
Asur ordusunun başkomutanı, Asur Kralı Sargon'un buyruğuyla gelerek Aşdot'a saldırıp kenti ele geçirdiği yıl RAB Amots oğlu Yeşaya aracılığıyla şöyle dedi: “Git, belindeki çulu çöz, ayağındaki çarığı çıkar.” Yeşaya denileni yaptı, çıplak ve yalınayak dolaşmaya başladı.
2 a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
3 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
RAB dedi ki, “Mısır'a ve Kûş'a belirti ve ibret olsun diye kulum Yeşaya nasıl üç yıl çıplak ve yalınayak dolaştıysa,
4 haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
Asur Kralı da Mısır'a utanç olsun diye Mısırlı tutsaklarla Kûşlu sürgünleri genç yaşlı demeden, çıplak ve yalınayak, mahrem yerleri açık yürütecek.
5 Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
Kûş'a bel bağlayan, Mısır'la övünen halk hüsrana uğrayacak, utanç içinde kalacak.
6 A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”
Bu kıyı bölgesinde yaşayanlar o gün, “Asur Kralı'nın elinden kurtulmak için yardımına sığındığımız, bel bağladığımız ulusların başına gelene bakın!” diyecekler, “Biz nasıl kurtulacağız?”

< Ishaya 20 >