< Ishaya 20 >
1 A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
L’année où Thartan vint à Azoth, envoyé par Sargon, roi d’Assyrie, assiégea Azoth et la prit,
2 a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
en ce temps-là, Yahweh parla par le ministère d’Isaïe, fils d’Amos, en disant: « Va, détache le sac qui couvre tes reins, et ôte les sandales de tes pieds. « Et il fit ainsi, marchant nu et déchaussé.
3 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
Et Yahweh dit: « De même que mon serviteur Isaïe a marché nu et déchaussé; étant pendant trois ans un signe et un présage, pour l’Égypte et pour l’Éthiopie;
4 haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
ainsi le roi d’Assyrie emmènera les captifs de l’Égypte, et les déportés de l’Éthiopie, jeunes gens et vieillards, nus et déchaussés, et les reins découverts, à la honte de l’Égypte.
5 Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
Alors ils seront consternés et confus, à cause de l’Éthiopie, qui était leur espoir, et de l’Égypte qui était leur sujet de gloire.
6 A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”
Et l’habitant de ce rivage dira en ce jour-là: Voilà ce qu’ est devenu celui en qui nous espérions; celui auprès de qui nous voulions fuir pour chercher du secours, pour être délivrés, des mains du roi d’Assyrie! Et nous, comment échapperons-nous? »