< Ishaya 20 >

1 A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
One year King Sargon of Assyria sent the chief commander of his army [to take his soldiers] to capture Ashdod [city in Philistia].
2 a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
At that time, Yahweh told me, “Take off the rough sackcloth that you have been wearing and take off your sandals.” [So] I did what he told me to do, and [then] I walked around naked and barefoot [for three years].
3 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
[Then] Yahweh said this [to the people of Judah]: “My servant Isaiah has been walking around naked and barefoot for the past three years. That is to show the terrible disasters that [I will cause the people of] Egypt and Ethiopia to experience.
4 haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
What will happen is that the [army of the] King of Assyria will [invade those countries and capture many of the people and] take them away as their prisoners. They will force all them, including both the young ones and the old ones, to walk naked and barefoot. They will [also] force them to have no clothes around their buttocks, which will cause [the people of] Egypt to be ashamed.
5 Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
Then the people of other countries who trusted that the armies of Egypt and Ethiopia would be able to help them will be very dismayed/confused and afraid/disappointed.
6 A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”
They will say, ‘We trusted that the armies of Egypt and Ethiopia [would help us and defend us, but they have been destroyed], so there is no way [RHQ] that we can escape from [being destroyed by the army of] the King of Assyria!’”

< Ishaya 20 >