< Ishaya 2 >

1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
Isto é o que Isaías, filho de Amoz, viu a respeito de Judá e Jerusalém.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
Acontecerá nos últimos dias, que a montanha da casa de Yahweh será estabelecida no topo das montanhas, e deve ser levantada acima das colinas; e todas as nações devem fluir para ele.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
Muitos povos devem ir e dizer, “Venha, vamos até a montanha de Yahweh”, para a casa do Deus de Jacob; e ele nos ensinará seus caminhos, e nós caminharemos em seus caminhos”. Pois a lei sairá de Sião, e a palavra de Yahweh de Jerusalém.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
Ele julgará entre as nações, e decidirá a respeito de muitos povos. Eles devem bater suas espadas em arados, e suas lanças em ganchos de poda. A nação não levantará espada contra a nação, nem devem aprender mais a guerra.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
Casa de Jacob, venha, e vamos caminhar na luz de Yahweh.
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
Pois você abandonou seu povo, a casa de Jacob, porque eles são preenchidos a partir do leste, com aqueles que praticam a adivinhação como os filisteus, e eles apertam as mãos com os filhos de estrangeiros.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
A terra deles está cheia de prata e ouro, nem há um fim de seus tesouros. Suas terras também estão cheias de cavalos, nem existe nenhuma ponta de suas carruagens.
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
A terra deles também está cheia de ídolos. Eles adoram o trabalho de suas próprias mãos, o que seus próprios dedos fizeram.
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
O homem é trazido para baixo, e a humanidade é humilhada; portanto, não os perdoe.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Entre na rocha, e se esconder na poeira, de antes do terror de Yahweh, e da glória de sua majestade.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
A aparência sublime do homem será reduzida, a arrogância dos homens será curvada, e Yahweh sozinho será exaltado nesse dia.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
Pois haverá um dia de Yahweh de Exércitos para todos os que se orgulham e são arrogantes, e por tudo isso é levantado, e deve ser levada a baixo
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
para todos os cedros do Líbano, que são altos e erguidos, para todos os carvalhos de Bashan,
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
para todas as altas montanhas, para todas as colinas que são erguidas,
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
para cada torre alta, para cada muro fortificado,
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
para todos os navios de Tarshish, e para todas as imagens agradáveis.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
A altura do homem deve ser curvada, e a arrogância dos homens deve ser reduzida; e Yahweh sozinho será exaltado naquele dia.
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
The os ídolos devem falecer por completo.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
Men deve ir para as cavernas das rochas, e para os buracos da terra, de antes do terror de Yahweh, e da glória de sua majestade, quando ele se levanta para sacudir a terra poderosamente.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
Naquele dia, os homens lançarão fora seus ídolos de prata e seus ídolos de ouro, que foram feitas para si mesmas para adorar, para as toupeiras e para os morcegos,
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
para ir para as cavernas das rochas, e para as fendas das rochas irregulares, de antes do terror de Yahweh, e da glória de sua majestade, quando ele se levanta para sacudir a terra com força.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Pare de confiar no homem, cuja respiração está em suas narinas; de que conta ele é?

< Ishaya 2 >