< Ishaya 2 >

1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
Det ord som Esaias, sønn av Amos, mottok i et syn om Juda og Jerusalem.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
Og det skal skje i de siste dager, da skal fjellet der Herrens hus står, være grunnfestet på toppen av fjellene og høit hevet over alle høider, og alle hedningefolk skal strømme til det.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
Og mange folkeslag skal gå avsted og si: Kom, la oss gå op til Herrens berg, til Jakobs Guds hus, så han kan lære oss sine veier, og vi ferdes på hans stier! For fra Sion skal lov utgå, og Herrens ord fra Jerusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
Og han skal dømme mellem hedningefolkene og skifte rett for mange folkeslag, og de skal smi sine sverd om til hakker og sine spyd til vingårdskniver; et folk skal ikke lenger løfte sverd mot et annet, og de skal ikke mere lære å føre krig.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
Jakobs hus! Kom, la oss vandre i Herrens lys!
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
For du har forkastet ditt folk, Jakobs hus, fordi de er fulle av Østerlands kunster og spår av skyene som filistrene, og mennesker av fremmed ætt drar de inn i landet i mengde.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
Deres land blev fullt av sølv og gull, og det er ingen ende på dets skatter; deres land blev fullt av hester, og det er ingen ende på dets vogner;
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
deres land blev fullt av avguder; de tilbeder sine henders verk, det deres fingrer har gjort.
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
Og mennesket blir bøiet, og mannen ydmyket - tilgi dem ikke!
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Gå inn i fjellet og skjul dig i støvet for Herrens gru og for hans høihets herlighet!
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
Menneskets stolte øine blir ydmyket, og mennenes stolthet blir bøiet, og Herren alene er høi på den dag.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
For Herren, hærskarenes Gud, har satt en dag til dom over alt stolt og høit og over alt ophøiet, så det blir ydmyket,
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
både over alle Libanons sedrer, de høie og ophøiede, og over alle Basans eker
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
og over alle de høie fjell og over alle de stolte høider
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
og over hvert høit tårn og over hver fast mur
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
og over alle Tarsis-skib og over alt som er fagert å skue.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
Og menneskets overmot blir bøiet, og mennenes stolthet blir ydmyket, og Herren alene er høi på den dag.
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
Og avgudene - med dem er det helt forbi.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
Og folk skal gå inn i fjellhulene og i jordens revner for Herrens gru og for hans høihets herlighet, når han reiser sig for å forferde jorden.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
På den dag skal menneskene kaste sine guder av sølv og gull, som de har gjort sig for å tilbede dem, bort til muldvarpene og flaggermusene
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
og gå inn i fjellkløftene og i berghulene for Herrens gru og for hans høihets herlighet, når han reiser sig for å forferde jorden.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Hold da op med å stole på mennesket, i hvis nese det bare er et pust! Hvad er han å akte for?

< Ishaya 2 >