< Ishaya 2 >

1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
Parole qu’a vue Isaïe, fils d’Amos, touchant Juda et Jérusalem.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
Et il arrivera dans les derniers jours que la montagne préparée pour la demeure du Seigneur sera établie sur le sommet des montagnes, et elle sera élevée au-dessus des collines, et tous les peuples y afflueront.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
Et beaucoup de peuples iront et diront: Venez, et montons à la montagne du Seigneur, et à la maison du Dieu de Jacob, et il nous enseignera ses voies, et nous marcherons dans ses sentiers; parce que de Sion sortira la loi, et la parole du Seigneur de Jérusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
Et il jugera les nations, et il convaincra beaucoup de peuples; et de leurs glaives ils forgeront des socs de charrue, et de leurs lances des faux; une nation ne lèvera pas le glaive contre une autre nation, elles ne s’exerceront plus au combat.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
Maison de Jacob, venez, et marchons à la lumière du Seigneur.
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
Car vous avez rejeté votre peuple, la maison de Jacob; parce qu’ils ont été remplis comme autrefois, qu’ils ont eu des augures comme les Philistins, et qu’ils se sont attachés à des enfants étrangers.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
Sa terre est remplie d’argent et d’or; et il n’y a pas de bornes à ses trésors;
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
Et sa terre est remplie de chevaux, et ses quadriges sont innombrables. Et sa terre est remplie d’idoles; ils ont adoré l’ouvrage de leurs mains, l’ouvrage qu’ont fait leurs doigts.
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
Et l’homme du peuple s’est courbé, et l’homme de condition est humilié; ne leur pardonnez donc point.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Entre dans la pierre, et cache-toi dans les creux de la terre, par la crainte du Seigneur et de la gloire de sa majesté.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
Les yeux altiers de l’homme du peuple ont été humiliés, et la fierté des hommes de condition sera abaissée; mais le Seigneur seul sera exalté en ce jour-là.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
Parce que le jour du Seigneur des armées éclatera sur tout esprit superbe et hautain et sur tout arrogant; et ils seront humiliés;
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
Et sur tous les cèdres du Liban, grands et élevés, et sur tous les chênes de Basan;
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
Et sur toutes les montagnes les plus hautes, et sur toutes les collines les plus élevées;
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
Et sur toute tour la plus élevée et sur toute muraille fortifiée;
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
Et sur tous les vaisseaux de Tharsis, et sur tout ce qui est beau à voir.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
Et l’orgueil des hommes du peuple sera abaissé, et la hauteur des hommes de condition sera humiliée, et le Seigneur seul sera élevé en ce jour-là;
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
Et les idoles seront entièrement brisées;
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
Et ils entreront dans les creux des rochers, dans les antres de la terre, par la frayeur du Seigneur, et à cause de la gloire de sa majesté, lorsqu’il se lèvera pour frapper la terre.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
En ce jour-là l’homme rejettera ses idoles d’argent et ses simulacres d’or, qu’il s’était faits pour les adorer, les taupes et les chauves-souris.
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
Et il entrera dans les fentes des pierres, et dans les cavernes des roches par la frayeur du Seigneur, et à cause de la gloire de sa majesté, lorsqu’il se lèvera pour frapper la terre.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Laissez donc l’homme dont le souffle est dans ses narines, parce qu’il a été réputé pour le Très-Haut.

< Ishaya 2 >