< Ishaya 2 >

1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
The thing that Isaiah son of Amoz hath seen concerning Judah and Jerusalem:
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
And it hath come to pass, In the latter end of the days, Established is the mount of Jehovah's house, Above the top of the mounts, And it hath been lifted up above the heights, And flowed unto it have all the nations.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
And gone have many peoples and said, 'Come, and we go up unto the mount of Jehovah, Unto the house of the God of Jacob, And He doth teach us of His ways, And we walk in His paths, For from Zion goeth forth a law, And a word of Jehovah from Jerusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
And He hath judged between the nations, And hath given a decision to many peoples, And they have beat their swords to ploughshares, And their spears to pruning-hooks, Nation doth not lift up sword unto nation, Nor do they learn any more — war.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
O house of Jacob, come, And we walk in the light of Jehovah.'
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
For Thou hast left Thy people, the house of Jacob. For they have been filled from the east, And [are] sorcerers like the Philistines, And with the children of strangers strike hands.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
And its land is full of silver and gold, And there is no end to its treasures, And its land is full of horses, And there is no end to its chariots,
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
And its land is full of idols, To the work of its hands it boweth itself, To that which its fingers have made,
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
And the low boweth down, and the high is humbled, And Thou acceptest them not.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Enter into a rock, and be hidden in dust, Because of the fear of Jehovah, And because of the honour of His excellency.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
The haughty eyes of man have been humbled, And bowed down hath been the loftiness of men, And set on high hath Jehovah alone been in that day.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
For a day [is] to Jehovah of Hosts, For every proud and high one, And for every lifted up and low one,
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
And for all cedars of Lebanon, The high and the exalted ones, And for all oaks of Bashan,
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
And for all the high mountains, And for all the exalted heights,
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
And for every high tower, And for every fenced wall,
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
And for all ships of Tarshish, And for all desirable pictures.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
And bowed down hath been the haughtiness of man, And humbled the loftiness of men, And set on high hath Jehovah alone been in that day.
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
And the idols — they completely pass away.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
And [men] have entered into caverns of rocks, And into caves of dust, Because of the fear of Jehovah, And because of the honour of His excellency, In His rising to terrify the earth.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
In that day doth man cast his idols of silver, And his idols of gold, That they have made for him to worship, To moles, and to bats,
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
To enter into cavities of the rocks, And into clefts of the high places, Because of the fear of Jehovah, And because of the honour of His excellency, In His rising to terrify the earth.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Cease for you from man, Whose breath [is] in his nostrils, For — in what is he esteemed?

< Ishaya 2 >