< Ishaya 2 >

1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
The word which Ysaie, the sone of Amos, siy on Juda and Jerusalem.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
And in the laste daies the hil of the hous of the Lord schal be maad redi in the cop of hillis, and schal be reisid aboue litle hillis. And alle hethene men schulen flowe to hym;
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
and many puplis schulen go, and schulen seie, Come ye, stie we to the hil of the Lord, and to the hous of God of Jacob; and he schal teche vs hise weies, and we schulen go in the pathis of hym. For whi the lawe schal go out of Syon, and the word of the Lord fro Jerusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
And he schal deme hethene men, and he schal repreue many puplis; and thei schulen welle togidere her swerdes in to scharris, and her speris in to sikelis, ether sithes; folk schal no more reise swerd ayens folk, and thei schulen no more be exercisid to batel.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
Come ye, the hous of Jacob, and go we in the liyt of the Lord.
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
Forsothe thou hast cast awei thi puple, the hous of Jacob, for thei ben fillid as sum tyme bifore; and thei hadden false dyuynouris bi the chiteryng of briddis, as Filisteis, and thei cleuyden to alien children.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
The lond is fillid with siluer and gold, and noon ende is of the tresouris therof; and the lond therof is fillid with horsis, and the foure horsid cartis therof ben vnnoumbrable.
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
And the lond therof is fillid with ydols, and thei worschipiden the werk of her hondis, which her fyngris maden;
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
and a man bowide hymsilf, and a man of ful age was maad low. Therfor foryyue thou not to hem.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Entre thou, puple of Juda, in to a stoon, be thou hid in a diche in erthe, fro the face of the drede of the Lord, and fro the glorie of his mageste.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
The iyen of an hiy man ben maad low, and the hiynesse of men schal be bowid doun; forsothe the Lord aloone schal be enhaunsid in that dai.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
For the dai of the Lord of oostis schal be on ech proud man and hiy, and on ech boostere, and he schal be maad low;
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
and on alle the cedres of the Liban hiye and reisid, and on alle the ookis of Baisan,
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
and on alle hiy munteyns, and on alle litle hillis, `that ben reisid;
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
and on ech hiy tour, and on ech strong wal;
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
and on alle schippis of Tharsis, and on al thing which is fair in siyt.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
And al the hiynesse of men schal be bowid doun, and the hiynesse of men schal be maad low; and the Lord aloone schal be reisid in that dai,
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
and idols schulen be brokun togidere outirli.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
And thei schulen entre in to dennes of stoonys, and in to the swolewis of erthe, fro the face of the inward drede of the Lord, and fro the glorie of his maieste, whanne he schal ryse to smyte the lond.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
In that dai a man schal caste awei the idols of his siluer, and the symylacris of his gold, whiche he hadde maad to hym silf, for to worschipe moldewarpis and backis, `ether rere myis.
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
And he schal entre in to chynnis, ethir crasyngis, of stoonys, and in to the caues of hard roochis, fro the face of the inward drede of the Lord, and fro the glorie of his mageste, whanne he schal ryse to smyte the lond.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Therfor ceesse ye fro a man, whos spirit is in hise nose thirlis, for he is arettid hiy.

< Ishaya 2 >