< Ishaya 2 >

1 Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
The things that Isaiah son of Amoz perceived in a vision, concerning Judah and Jerusalem.
2 A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
It will be in the last days that the mountain of Yahweh's house will be established as the highest of the mountains, and it will be raised up above the hills, and all the nations will flow to it.
3 Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
Many peoples will come and say, “Come, let us go up to the mountain of Yahweh, to the house of the God of Jacob, so he may teach us some of his ways, and we may walk in his paths.” For out of Zion will go the law, and the word of Yahweh from Jerusalem.
4 Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
He will judge between the nations and will render decisions for many peoples; they will hammer their swords into plowshares, and their spears into pruning hooks; nation will not lift up sword against nation, nor will they train for war any longer.
5 Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
House of Jacob, come, and let us walk in the light of Yahweh.
6 Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
For you have abandoned your people, the house of Jacob, because they are filled with customs from the east and they practice divination like the Philistines, and they shake hands with sons of foreigners.
7 Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
Their land is full of silver and gold, and is there no limit to their wealth; their land also is full of horses, nor is there limit to their chariots.
8 Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
Their land also is full of idols; they worship the craftsmanship of their own hands, things that their own fingers have made.
9 Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
The people will be bowed down, and individuals will fall down; therefore do not raise them up.
10 Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
Go into the rocky places and hide in the ground from the terror of Yahweh and from the glory of his majesty.
11 Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
The lofty gaze of man will be brought low, and the pride of men will be brought down, and Yahweh alone will be exalted on that day.
12 Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
For there will be a day of Yahweh of hosts against everyone who is proud and raised up, and against everyone who is arrogant—and he will be brought down—
13 domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
and against all the cedars of Lebanon that are high and lifted up, and against all the oaks of Bashan.
14 domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
That day of Yahweh of hosts will be against all the high mountains, and against all the hills that are lifted up,
15 domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
and against every high tower, and against every impregnable wall,
16 domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
and against all the ships of Tarshish, and against all beautiful sailing vessels.
17 Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
The pride of man will be brought low, and the haughtiness of men will fall; Yahweh alone will be exalted on that day.
18 za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
The idols will completely pass away.
19 Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
Men will go into the caves of the rocks and the holes of the ground, from the terror of Yahweh, and from the glory of his majesty, when he rises to terrify the earth.
20 A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
On that day people will throw away their idols of silver and of gold that they have made for themselves to worship—they will throw them away to the moles and bats.
21 Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
The people will go into the crevices in the rocks and into the clefts of the ragged rocks, from the terror of Yahweh and from the glory of his majesty, when he rises to terrify the earth.
22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Stop trusting in man, whose life-breath is in his nostrils, for what does he amount to?

< Ishaya 2 >